Skip to main content

Posts

Showing posts from 2020

Kwalejin Ilmi Ta Sokoto Za Ta Koma Jami'ar Ilmi Ta Sokoto - Tambuwal

Gwanan jahar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya lashi takobin ganin kwalejin Ilmi ta Shehu Shagari ta koma Jami'ar Horas da Malamai da Fannonin Ilmi Ta Jahar Sokoto. Ya fadi hakan yau litinin a lokacin bukin cikar kwalejin shekaru 50 da kafuwa, karo na 22. Ya yi karin hasken cewa ganin yadda ya dauki sha'anin ilmi da muhimmanci da ma yadda ya ke ware masa kaso mafi tsoka a kasafin kudin gwamnatinsa, zai gana da masu ruwa da tsaki a fannin ilmi da ma mai alfarma Sarkin musulmi don neman shawara akan wannan batu. Ya kara da cewa zai kara ginawa kwalejin karin dakunan kwanan dalibai, domin saukake matsalar cin koso. To amma kuma, wasu da TANTABARA ta zanta da su, na kallon batun a matsayin irin alkawurran  da ya ta bayi na samar da karin Sassan nazarin ilmin kimiyya da liktanci a Jami'ar Jahar Sokoto,  tun shekaru uku da suka gabata, amma suka zama durmukyal da suka ce kalamai ne na rufa ido kawai da ya saba da su. To, sai dai aikin gina asibitin koyarwar jami'ar

An Rufe Makarantu Da Wuraren Holewa A Najeriya

Sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya Boss Mustapha ne ya bayar da umurnin a jiya, cewa dukan makarantu da wuraren shakatawa za su kasance a rufe har tsawon makonni biyar. Gwamnatin ta kuma bayar da umurnin ma'aikata daga mataki na 12 zuwa kasa su yi zaman su a gida, in ban da ma su aikin gaggawa, kamar jami'an kiyon lafiya da sauran su. Wannan matakin ya biyo bayan yadda annobar korona ke ci gaba da hayyaka a Najeriya. Haka ma an jiyo ministan lafiyar kasar Osagie Ehanire na bayar da umurnin sake bude cibiyoyin killace wadanda suka kamu da cutar. Tuni dai wasu jahohin kasar da suka hada da Legas, Kaduna da Imo suka bayar da damar rufe makarantu tare da gindaya dokoki da ka'idojin yaki da cutar, ta hanyar rufe wuraren rawa da takaita zirga-zirga da kayyade lokacin halartar wuraren ibada da ma saka takunkumi.

Sabuwar Kwayar Cutar Korona Ta Soma Yaduwa

A farkon makon nan a ka gano wata nau'in kwayar cutar korona da ta sha bamban da wacce aka sani. Ita dai wannan sabuwar kwayar cuta ta bulla ne a kasar Burtaniya, in da ta yi nasarar mamaye birnin Landan da gasbascin kasar a yankunan Surrey, Essex, Backshire, Backinghamshire Kent da sauran su. Firaminstan kasar Boris Johnson ya ce a halin da ake ciki yanzu, kwayar cutar na bazuwa ne cikin sauri fiye da ta farko; wanda yanzu haka ta ke kashi 70 cikin dari a mizanin yaduwa. Masana kiyon lafiya a duniya sun bayyana cewa, ba Burtaniya kadai wannan sabuwar korona ta bulla ba, har da da Afirka ta kudu da ma sauran sassan duniya kawai dai ba a kai ga farga da hakan ba ne. A cewar su, Burtaniya dai ce ta yi kwakkafin gano ta saboda tsananin bincike da gwajin da ta fi kowace kasa yi kan wannan cuta. Tuni dai kasashen duniya da suka hada da Jamus, Faransa, Italiya, Austireliya, Iceland, Spaniya, Saudiyya da sauran su, suka dakatar da zirga zirgar jiragen sama tsakaninsu da kasar

Da Dumi Dumi - Daliban Makarantar Kimiyya Ta Kankara Sun Iso Gida

Yanzu yanzun nan daliban da aka sace a Makarantar Kimiyya da Fasaha ta Kankara da ke jahar Katsina suka iso gida. Yaran su kimanin 340 cikin rakiyar jami'an tsaron soji da 'yan sanda, sun iso fuskokinsu cike da annuri, koda yake dukan su sun yi butu-butu da kura alamar wahala. Shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi waya da gwamnan jahar Katsina Aminu Bello Masari in da ya taya shi murnar samun nasarar ceto yaran. An dai sace yaran a ranar jumu'a da dare da ta gabata a wata makarantar kwana da ke karamar hukumar Kankara a jahar ta Katsina. Gwamnatin jahar ba ta yi cikakken bayanin yadda aka karbo yaran ba, ko da ya ke a bidiyon da kungiyar Boko Haram ta fitar da rana an ji wani mai garkuwa da yaran na fadin suna tattaunawa da gwamnati don karbar kudin fansa.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Kungiyar Boko Haram Ta Saki Bidiyon Yaran Da Aka Sace A Katsina

Kungiyar Boko Haram ta saki wani faifan bidiyo da ke nuna yaran nan daliban makarantar kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina, kwanaki biyar da sace su. A cikin bidiyon an ga wani yaro mai kimanin shekaru sha biyar na magana cikin Hausa: "Don Allah ina rokon gwamnati da kada ta yi amfani da duk wasu 'yan sa kai, a rufe dukan makarantu. Kuma sojojin da ke tafe don taimakonmu don Allah su koma, ba za su iya yi wa (mayakan) kome ba". In ji yaron. A can bayan yaron an ga wasu yara kanana masu yawan gaske da ake umurta da su zauna, kuma da ba su fi shekara goma goma ba, suna kuka tare da rokon a taimaka a cece su daga hannun mayakan. Faifan bidiyon mai tsawon minti daya ya nuna yaran cikin kura da alamar gajiya a tattare da su, sakamakon tafiya mai nisa a kasa. Ana kuma jin muryar daya daga 'yan bindigar na gargadin gwamnati da kada ta dauki kowane matakin amfani da karfi. Yana mai jaddada cewa yaran na cikin koshin lafiya. A ranar jumu'ar da ta gabata ne maharan suka y

Da Dumi Dumi - An Bude Iyakokin Najeriya Hudu

Gwamnatin Najeriya ta bayar da umurnin bude kan iyakokita a yau din nan, da suka hada da ta Sokoto a garin Illela da Seme daga kudu maso yamma da Mfun ta kudu maso kudu da kuma ta Maigatari a jahar Katsina. Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya bayar da wannan umurnin ta hannun mai ba shi shawara kan shafukan sada zumunta Bashir Ahmad, wanda ya wallafa a shafinsa na tweeter. An dai kwashe fiye da shekara daya iyakokin na kulle, a bisa dalilan tsaro da hana fasa kwabrin shinkafa da miyagun kwayoyi zuwa cikin kasar. 'Yan Najeriya da dama ne suka shiga halin matsi sakamakon rufe kan iyakokin, in da tsada da karancin kayan masaruhi suka kai wani mataki da ba a saba ganin irin sa ba a Najeriya. Da dama daga kasashe makwabta da suka hada da Gana da Jamhuriyar Nijar da Kamaru, sun sha matsin lamba da a bude iyakokin domin samun damar huldar cinikayya tsakaninsu da Najeriya. Hasalima ana ganin wannan na daya daga dakilan da suka haifar da rashin jituwa tsakanin Najer

'Yan Bindigar Da Suka Sace Dalibai A Jahar Katsina Sun Ce Kada Su Sake Jin Shawagin Jirgin Sama Kusa Da Su

A jiya ne daya daga iyayen yaran da mayakan suka dauke ya sanar da hukumomi cewa 'yan bidigar sun kira shi ta waya, in da suka yi gargadin cewa a tabbatar wani jirgin saman yaki bai sake ci gaba da shawagi a kusa da in da su ke ba, idan ba haka ba za su dauki matakin da ya yi mu su daidai. Rahotanni da ke fitowa yanzu haka na cewa maharan sun tafiyar da ta kai dazukan jahar Zamfara da yaran, kuma sun fara tattaunawa don neman kudin fansa kafin su kai ga sakin su. A yau gwamnan jahar Katsina Aminu Bello Masari, ya sanar da manema labarai cewa, an kai ga gano yara 17 daga cikin wadanda suka tarwatse a daji, ina da tun jiya aka sada su da iyayensu. A ranar jumu'a da ta gabata dai ne wasu 'yan bindiga da ba a kai ga ganowa ba suka yi awon gaba da yaran, koda ya ke jiya litinin shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau, ya bayyana cewa su suka sace yaran.

Duk Layin Kiran Da Ba A Hada Da Lambar Katin Dan Kasa Ba Za A Rufe Shi - Pantami

Ministan Sadarwar Najeriya Dakta Isah Ali Pantami ya nanata matsayarsa na tabbatar da an dakatar da sayar da layukan kira tare da tsayar da yi wa sabbin layukkan rajista. Ya bayyana hakan a lokacin taron da ya gudanar da masu ruwa da tsaki a bangaren sadarwa, da suka hada da Hukumar Da Ke Sanya Ido Kan Harkokin Sadarwa NCC da Hukumar Bunkasa Fasahar Zamani Ta Kasa NITDA da Hukumar Samar Da Katin Shaidar Zama Dan Kasa NIMC da sauran kamfunnan sadarwar wayoyin hannu na   MTN, Glo, Airtel, Etisalat ko 9mobile  da sauran su. A wajen taron ministan sadarwar ya umurci kamfunnan su kiyaye dokoki da sharuddan da aka gindaya, kazalika dukan kamfunnan sadarwar wayoyin hannu su tilasta duk mai amfani da layukansu da ya hada layinsa na kira da lambar katinsa na shaidar zama dan kasa domin tabbatar da shi. Sun kuma tattauna akan cewa za a soma wannan daga yau din nan laraba 16 ga Disamban 2020 zuwa ranar laraba 30 ga wannan watan na Disamban 2020, wanda daga nan za a rufe layin duk wan

Jahohin Zamfara, Kaduna Da Jigawa Sun Bada Umurnin Rufe Makarantun Boko

Jahar Jigawa ta bayar da umurnin rufe makarantun Boko daga yau din nan laraba har zuwa wani lokacin da ba a bayyana ba. Jahohi irin su Kaduna, Kano da Sokoto sun bi sahu. Wannan mataki dai a cewar gwamnatin jahar jigawa na da alaka ne da matsalar ci gaba da yaduwar annobar korona. Amma da dama na ganin hakan bai rasa nasaba da harin da 'yan bindiga suka kai a wata makarantar kimiyya ta kwana da ke Kankarar jahar Katsina ranar jumu'ar da ta gabata ne, in da ake jin sun yi awon gaba da dalibai kusan 500. A jiya kungiyar Boko Haram ta fito ta yi ikirarin daukar alhakin sace yaran, abinda ya jefa tsoro da zullumi a zukatan al'umma.

Sanwolu Da El-Rufai Sun Killace Kan Su Saboda Covid-19

Gwamnan jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i ya kebe kan sa saboda wani daga cikin iyalinsa da hadimansa sun kamu da cutar korona. Gwamnan ya bayyana hakan a shafinsa na tweeter, in da ya ce a gobe lahadi zai je asibiti don auna shi a tabbatar idan har yana dauke da ita. Shi ma gwamnan jahar Legas, Babajide Sanwolu ya bayyana killace kansa sakamakon samun wasu na kusa da shi dauke da cutar. Sanwolu ya bayyana cewa wajibi ne ya kebe kan sa kafin a gudanar da gwaji, gudun kada idan ya na dauke da ita ya yadawa wasu makusanta. Jahar Legas dai na sahun gaba daga jerin masu dauke da cutar a Najeriya. Duka jahohin biyu sun yi fama da dokar kulle a watannin baya lokacin da annobar ta yi kamari. Kwanaki uku da su ka gabata an jiyo gwamnan jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i, na barazanar kulle jahar muddin jama'a suka ci gaba da kin bin ka'idojin yaki da cutar korona da aka san da su.

Mutum 64 Sun Kamu Da Korona A Kaduna - El-Rufa'i

Gwamnatin jahar Kaduna ta fitar da sanarwar cewa annobar korona ta sake dawowa a jahar. Gwamnatin jahar ta tabbara da samun sabbin kamuwa da cutar har mutum 64, wanda a cewar ta tuni su ma a ka kebe su. An kuma jiyo gwamnan jahar Malam Nasiru El-Rufa'i, na cewa muddin jama'ar jahar suka ci gaba da yin biris da dokokin da aka shata musu to babu makawa gwamnatin za ta sake kulle su ruf har sai lokacin da annobar Covid-19 din ta lafa. Gwamnan ya ce yana mamakin yadda al'umma ke watsi da ka'idojin da tuni aka san da su, na rage cin koso da sanya takunkumi da kuma yawaita wanke hannuwa. Jahar Kaduna na cikin jahohin da suka fuskanci dokar kulle sakamkon barkewar annobar ta korona a watannin baya. To sai dai wannan gargadi na gwamnatin jahar ya gamu da suka, musamman ga wadanda ke kallon kalaman a matsayin na 'yan boko.

Maina Ya Kife A Kotu

 Tsohon shugaban kwamitin hana badakala a hukumar fansho ta kasa Abdulrasheed Maina, ya fadi a kotun birnin tarayya a Abuja, daidai lokacin da ake tsaka da yi masa shari'a. Tsohon shugaban kwamitin dai ana tuhumar sa ne da badakalar da ta danganci batar da kimanin naira biliyan biyu sa'adda da ya ke jagorancin kwamitin. Tun daga lokacin da aka kai shi kotu Maina ya yi batan dabo bayan da ya samu beli. Bayan kwashe tsawon lokaci ana neman sa daga bisa ni an yi nasarar gano shi a kasar Jamhuriyar Nijar. Wannan al'adar faduwa a gaban kwamitocin bincike ba bakuwa ba ce a Najeriya, in da ko watannin baya shugaban kwamitin Hukumar Raya Yankin Naija Delta (NDDC) farfesa Podei ya yi zaman tsumma a kwando, lokacin da yake amsa bahasi a gaban kwamitin majalisar wakilai na kasa dangane da badakalar da ake zargin sa da hannu na karkata kwangiloli da kudaden hukumar zuwa wata hanya daban.

Kotu Ta Aminta Da Rataye Maryam Sanda

Yau din nan kotun birnin tarayya Abuja ta tabbatar da hukunci da kotun baya ta yanke na rataye Maryam Sanda. Kotun ta bayyana cewa hukuncin da aka yanke ma ta tun da farko babu kuskure cikin sa saboda haka ta bayar da umurnin gaggauta rataye ta. An dai samu Maryam sanda da laifin kashe mijinta har lahira ta hanyar daba masa wuka. Amma ta daukaka kara kan hukuncin da aka yanke ma ta a watan Janairun wannan shekara ta 2020.

Barayi Sun Yiwa Ofishin Jaridar Daily Star Nigeria Kaf

A yau da rana wasu gungun barayi da ba a kai ga ganowa ba sun kai samame ofishin jaridar Daily Star Nigeria da ke jahar Sokoto. Babban editan jaridar, Dr. Mansur Isah Buhari ya tabbatar da wannan lamari, in da ya ce barayin sun yi awon gaba da wasu muhimman kaya da suka hada da kananan kwamfutoci, da akwatin talabijin da ma wasu kudaden da ba a bayyana adadinsu ba kawo yanzu. Dr. Mansur ya ce, "kamar yadda al'adar ofishinmu ta ke, wakilanmu na wajen nemo labarai ni kai na ma na dan fita bana wajen, lokacin da barayin suka auni hakan tare da fasa kofar ofishin in da suka wawushe kome". Jaridar Daily Star Nigeria dai na cikin na gaba gaba daga cikin jerin jaridun yanar gizo da ake da su a Nijeriya yanzu haka.

Kungiyar Boko Haram Ta Dauki Alhakin Kisan Manoma 78 A Jahar Borno

A cikin wani sabon faifan bidiyo da kungiyar ta fitar a yau, shugabanta Abubakar Shikau ya ce su ne suka aikata kisan manoman a garin Zabarbarin jahar Borno. Shikau ya ce sun yi wannan ne saboda fansa game da abinda sojojin Najeriya ke yi musu da taimakon al'umma. In da ya ci gaba da cewa da dama daga mazauna yankunan na tseguntawa jami'an tsaro maboyarsu, wanda hakan kan kai ga kama su. Shugaban kungiyar ya ce, sun dauki matakin yanka duk wanda ya ci gaba da tseguntawa jami'an sojoji sirrinsu. Har kawo yanzu dai gwamnatin Najeriya ba ta mayar da martani kan wannan sabuwar sanarwa da kungiyar Boko Haram ta fitar ba.

Gwamnatin Tambuwal Na Shirin Ba Da Mamaki

Gwamnatin jahar Sokoto ta yunkoro wajen samar da ayukkan raya gari, tun daga soma aikin Asibitin Koyarwa ta Jami'ar Jahar Sokoto da kuma Makarantar 'Yan Mata da ke garin Kasarawa galibin mazauna jahar ke ganin cewa an soma samun sauyi. Ganin yadda aka soma wasu ayukan da aka yi shekaru ana jira. Kuma cikin sauri da kamala. Tun lokacin zuwan gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal a 2015, galibin jama'a ke fadin albarkacin baki ganin gudanar da ayukkan kamar da wasa. To sai dai kuma, gwamnatin ta bayar da kwangiloli da suka hada da gina gadojin sama guda biyu da aka ce za a gina nan take. Kazalika da samar da filin wasa katafare da aka ambata da sauran su. TANTABARA ta zanta da wasu mazauna yankunan da ake ayukan in da suka shaida mata cewa suna murna da samar da ci gaban idan har ya tabbata. Haka ma wasu da dama sun soma samun hanyar abin kaiwa bakin salati daga soma ayukkan, inda suka kakkafa sana'o'insu a wuraren. A ziyarar da TANTABARA ta kai wura

'Yan Majalisa Sun Nemi Buhari Ya Yi Garambawul Ga Manyan Jami'an Sojoji

'Yan majalisar dattawan Najeriya sun bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake lale akan sha'anin tsaro. 'Yan majalisar dai sun nemi Buhari ya yiwa manyan hafsoshin sojin kasar garambawul, tare da sanya sabbin jini.  Sanata Kashim Shatima ya bayyana damuwarsa tare da shawartar shugaban kasa da ya sa a yi bincike kan lamarin tare da tabbatar da an magance matsalar tsaro a yankin arewa maso gabas. Shatima ya ce "wannan lamari ne da ya zama wajibi a dauki tsattsauran mataki game da shi". Shi ma sanata Adamu Aleiro daga jahar Kabi, a wani sako da ya aike a rubuce, ya bayyana cewa, "bai kamata shugaba Buhari ya aike da tawaga a jahar Borno don yin jaje ba, da kan sa ya dace ya je". Aleiro ya kuma shawarci shugaba Buhari da yayi garambawul ga manyan jami'an sojoji Najeriya tare da maye su da sabbin jini. Rikicin Boko Haram dai ya kwashe shekaru 11 yana addabar yankin arewa maso gabascin Najeriya, kuma yayi sanadiyyar hallakar dubban rayuka

Rikicin Jam'iyyar PDP A Kudu Maso Yamma

   Rikicin jam’iyar PDP a yankin kudu maso yammacin Najeriya na cikin kwale-kwale tun bayan da aka zabi gwamnan jahar Oyo Seyi Makinde jam’iyar PDP ke ganin ya na uwa da makarbiya a dukan lamurran da suka shafi jam’iyar, abinda suka ce na neman mayar da hannun agogo baya; kuma lamarin da wasu shuwagabannin jam’iyyar ke ganin shisshigi ne da kuma tare hanyar wasu. A baya bayan nan gwamna Makinde ya dinga kai kawo a rikicin jam’iyar a jahar Ikiti da ya ce neman sulhu ne da shiga tsakani, amma hakan ya kai ga musayar yawu tsakaninsa da gwamnan jahar Peter Fayose na lokacin, wanda ke yiwa gwamnan jahar Oyon kallon mai goyon bayan Sanata Abiodun Olujinmi da ya tsaya takara tare da shi. A halin yanzu an ji gwamnan na jahar Oyo na kurari da nuna goyon baya akan shari'ar da ake yi wa Fayose, in da Makinde ke ganin ya dace Hukumar Yaki da Zarmiyar Dukiyar Al’umma ta EFCC ta ci gaba tuhumar tsohon gwamnan jahar Ikitin. Rahotanni sun ce an jiyo shi ya na cewa, duk

Shin Kuna Da Labarin Al'ajubban Duniya 7

 Shin kun taba jin labarin abubuwan al'ajabi guda 7 da ake kira Seven Wonders of the World a turance? Idan ba ku taba ba to yau zamu fara kawo mu ku bayani game da su, inda zamu soma da Dalar Giza da ke kasar Misira. Ita dai wannan dala da kuke ganin hotonta a kasa, na da matukar ban mamaki; an gina ta ne dubban shekaru da suka gabata, tun a wajajen 2580 - 2560 kafin haihuwar annabi Isa. Tarihi ya nuna wani basaraken Misira mai suna Fir'auna Khufus ne ya gina ta, a matsayin babbar makabartar bizne manyan sarakunan Masar da aka fi sani da Fir'aunoni, da ma manyan tajiran wancan lokaci. Tsawonta ya kai mita 146.7 wato kafa 481 kenan. Haka ma fadin dalar Giza ya kai mita 230.34 ko kuma kafa 455 kenan. An yi amfani da birki ko bulo na manya manyan duwatsu da girmansu zai kai na mota marsandi, wanda miliyoyin bayi suka turo daga wurare masu nisan gaske zuwa inda aka gina dalar. Tarihi ya nuna an dauki tsawon shekaru 20 ana gina wannan dala kuma a halin yanzu tana da shekaru 3,80

Gwamnatin Najeriya Ta Shirya Da ASUU

 An kai matsaya tsakanin Kungiyar Malaman Jami'o'i ASUU in da gwamnatin tarayya ta amince da bukatunsu. A jiya jumu'a dai ne suka yi wani zama don ganin malaman sun janye yajin aikin da ya dauki watanni bakwai ana yi. A yanzu dai gwamntin Najeriya ta amince da cire malaman daga tsarin albashi na IPPIS wanda suka jima suna turjiya akai, kuma za ta biya malaman albashin duk watannin da su ke bi. Haka ma ministan kwadagon Najeriya Cris Ngige ya tabbatarwa manema labarai cewa, za a karawa malaman jami'ar alwus da zai kai naira biliyan 35 sabanin yadda yake a da na biliyan 30. Ngige ya kuma ce za a ci gaba da tattaunawa kan sabon tsarin albashi na UTAS muddin an kammala tsara shi. A nasu bangare kungiyar malaman jami'o'in sun yi maraba da wannan yunkuri, in da ake ganin matakin ga alama zai iya kawo karshen dogon yajin aikin da aka dade ana yi.

Ba Zamu Bar Korona Ta Haifar Muna Da Bashin Da Zai Ruguza Mu Ba - Antonio Gutarres

 A yau jumu'a sakataren Majalisar Dunkin Duniya, Antonio Gutarres ya bayyana cewa dimbin bashin da annobar korona ta jefa duniya ya wuce misali, baya ga yunwa da tashin hankali da sauran matsaloli da ke addabar kasashe musamman masu tasowa. Yana wadannan kalamai ne daidai lokacin da a karshen makon nan ake shirin gudanar da taron kolin kasashe ashirin masu karfin tattalin arziki na duniya da aka fi sani da G-20.  Ya ce bai kamata bashi ya zama tarnaki ga ci gaban duniya ba. Ana ganin yana wannan magana ne da manufar tursasa manyan kasashe masu arziki da su yi sassauci ga matalautan kasashe a bangaren da ya shafi dimbin bashin da ake bin su. Gutarres ya ce, "kasashe masu arziki kamar Amurka da China ya dace su samar da sassauci da daidaito ga kasashe masu tasowa, domin taimaka mu su farfadowa". Ya yi nuni da irin illar da kin hakan za ta iya haifarwa duniya nan gaba, "kusan hanyar samar da kandagarkin Covid-19 ba ta wuce ta kudi ba, kenan bai dace a ce duk rana ta All

Saudiyya Ta Harbo Jirgin Saman 'Yan Tawayen Houthi

 Kasar Saudiyya ta yi nasarar harbo wani jirgi maras matuki da aka gano na mayaka 'yan tawayen Houthi ne da ke Yamen. Kasar ta Saudiyya dai ta ce tuni mayakan 'yan tawayen da suka dade suna gwabza fada da gwamnatin Yamen da Saudiyyar ke marawa baya, suka sha alwashin kai ma ta hari. Jirgin maras matuki ya durfafi Saudiyya ne kafin daga bisani gungun kawancen da take dafawa yayi nasarar harbo shi.

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

Mai Tsaron Lafiyar Kakakin Majalisar Wakilai Ta kasa Ya Harbe Mai Sayar Da Jarida

 A jiya da yammaci ne dai lamarin ya faru in da daya daga jami'an da ke kare lafiyar kakakin majalisar wakilai na kasa, Femi Gbajabiamila ya yayi harbin da yayi sanadiyyar mutuwar wani mai tallar jarida. Gbajabiamila ya wallafa a shafinsa na tweeter cewa, yana kan hanyar dawowa ya tsaya wajen don gaisawa da mutane, to sai wasu gungun mutane suka taso masa abinda ya sa masu tsaron lafiyarsa suka yi harbi, wanda ta kai ga samun daya daga cikin masu sayar da jaridun da ke wurin. Bayanan da TANTABARA ta samu na cewa an dakatar da jami'n da ake zargi da yin harbin, har sai an kammala bincike. Galibin lokuta ana zargin jami'an tsaron Najeriya da yin harbin da kan jawo hallakar mutane, wanda ko kwanan baya irin haka ta faru a Kano in da ake zargin jami'an tsaron 'yan sanda da hallaka wasu mutane uku bisa harbin da ake zargin na kuskure ne.

Gwamnatin Nijeriya Ta Karyata Kashe Masu Zanga-Zanga A Lekki

 Minjstan watsa kabaran Najeriya Alhaji Lai Muhammad ya karyata rahoton kafar yada labaran CNN da ke cewa sojoji sun harbi da dama daga masu zanga-zangar Endsars a Lekki ta jahar Legas. Ministan ya shaidawa manema labarai hakan inda ya ce gwamnatin Najeriya za ta dauki mataki kan batun, da ya hada da rubutawa kafar ta CNN wasika akan ta karyata rahoton ko kuma duk abinda ya biyo baya kada su yi nadamarsa. A cikin wani bidiyo da kafar ta watsa an nuna sojoji na harbin masu zanga-zangar da harsashe na kwarai; har ma an ga wasun da aka harba kwance cikin jini. To sai dai tun a watan Oktoban da lamarin ya faru, hukumomin kare hakkin dan Adam da suka hada da Amnesty International suka fitar da rahotannin zargin harbin bindigar da ake alakantawa da jami'an soji.

LABARI DA DUMI DUMI

  Rundunar sojojin Najeriya ta samu nasarar tarwatsa 'yan bindigar da suka tare hanyar Kaduna zuwa Abuja. A kwanan nan 'yan bindigar masu garkuwa da mutane sun kashe akalla mutum 15 kan hanyar tare da jikkata da dama. Rundunar sojan ta bakin jami'in hulda da manema labarai Manjo Janar Enenche ta ce ta samu rahoton asiri ne dangane da 'yan ta'addan.

AN KUSA SHAWO KAN CUTAR COVID-19

 Rahotanni da ke fitowa yanzu haka sun bayyana cewa sabbin magungunnan rikagakafin cutar korona na nuna alamaun tasiri cikin gaggawa.  Kamfunnan Pfizer da BioNtech ne sahun gaba wajen samar da maganin, wanda an yi gwajinsa akan kimanin mutum 43,000 a kasashen duniya daban-daban tare da lura da cewa yana kashe cutar da kashi 94.5 kuma ba hi da illa. Masana kiyon lafiya a duniya dai sun bayar da shawarar ci gaba da amfani da rigakafin, sakamakon amanna da suka yi da shi. Ana sa ran samar da adadi mai yawa da zai wadaci al'ummar duniya nan da karshen shekara mai kamawa ta 2021, wanda ake muradin samun kimanin biliyan daya da doriya. Annobar korona da ta bulla tun a farkon 2020 ta kawowa duniya koma baya, wanda galibin kasashe masu karfin tattalin arziki suka gamu da cikas a bangaren tattalin arzikin, wanda ya shafi sassa da dama da suka hada da suhuri da yawo bude ido da ma cinikayya. Wannan yunkurin samar da rigakafin dai ana daukar sa a matsayin sabon kandagarki ga annibar Covid-19.