Skip to main content

Posts

Showing posts from December 16, 2020

Da Dumi Dumi - An Bude Iyakokin Najeriya Hudu

Gwamnatin Najeriya ta bayar da umurnin bude kan iyakokita a yau din nan, da suka hada da ta Sokoto a garin Illela da Seme daga kudu maso yamma da Mfun ta kudu maso kudu da kuma ta Maigatari a jahar Katsina. Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya bayar da wannan umurnin ta hannun mai ba shi shawara kan shafukan sada zumunta Bashir Ahmad, wanda ya wallafa a shafinsa na tweeter. An dai kwashe fiye da shekara daya iyakokin na kulle, a bisa dalilan tsaro da hana fasa kwabrin shinkafa da miyagun kwayoyi zuwa cikin kasar. 'Yan Najeriya da dama ne suka shiga halin matsi sakamakon rufe kan iyakokin, in da tsada da karancin kayan masaruhi suka kai wani mataki da ba a saba ganin irin sa ba a Najeriya. Da dama daga kasashe makwabta da suka hada da Gana da Jamhuriyar Nijar da Kamaru, sun sha matsin lamba da a bude iyakokin domin samun damar huldar cinikayya tsakaninsu da Najeriya. Hasalima ana ganin wannan na daya daga dakilan da suka haifar da rashin jituwa tsakanin Najer

'Yan Bindigar Da Suka Sace Dalibai A Jahar Katsina Sun Ce Kada Su Sake Jin Shawagin Jirgin Sama Kusa Da Su

A jiya ne daya daga iyayen yaran da mayakan suka dauke ya sanar da hukumomi cewa 'yan bidigar sun kira shi ta waya, in da suka yi gargadin cewa a tabbatar wani jirgin saman yaki bai sake ci gaba da shawagi a kusa da in da su ke ba, idan ba haka ba za su dauki matakin da ya yi mu su daidai. Rahotanni da ke fitowa yanzu haka na cewa maharan sun tafiyar da ta kai dazukan jahar Zamfara da yaran, kuma sun fara tattaunawa don neman kudin fansa kafin su kai ga sakin su. A yau gwamnan jahar Katsina Aminu Bello Masari, ya sanar da manema labarai cewa, an kai ga gano yara 17 daga cikin wadanda suka tarwatse a daji, ina da tun jiya aka sada su da iyayensu. A ranar jumu'a da ta gabata dai ne wasu 'yan bindiga da ba a kai ga ganowa ba suka yi awon gaba da yaran, koda ya ke jiya litinin shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau, ya bayyana cewa su suka sace yaran.

Duk Layin Kiran Da Ba A Hada Da Lambar Katin Dan Kasa Ba Za A Rufe Shi - Pantami

Ministan Sadarwar Najeriya Dakta Isah Ali Pantami ya nanata matsayarsa na tabbatar da an dakatar da sayar da layukan kira tare da tsayar da yi wa sabbin layukkan rajista. Ya bayyana hakan a lokacin taron da ya gudanar da masu ruwa da tsaki a bangaren sadarwa, da suka hada da Hukumar Da Ke Sanya Ido Kan Harkokin Sadarwa NCC da Hukumar Bunkasa Fasahar Zamani Ta Kasa NITDA da Hukumar Samar Da Katin Shaidar Zama Dan Kasa NIMC da sauran kamfunnan sadarwar wayoyin hannu na   MTN, Glo, Airtel, Etisalat ko 9mobile  da sauran su. A wajen taron ministan sadarwar ya umurci kamfunnan su kiyaye dokoki da sharuddan da aka gindaya, kazalika dukan kamfunnan sadarwar wayoyin hannu su tilasta duk mai amfani da layukansu da ya hada layinsa na kira da lambar katinsa na shaidar zama dan kasa domin tabbatar da shi. Sun kuma tattauna akan cewa za a soma wannan daga yau din nan laraba 16 ga Disamban 2020 zuwa ranar laraba 30 ga wannan watan na Disamban 2020, wanda daga nan za a rufe layin duk wan

Jahohin Zamfara, Kaduna Da Jigawa Sun Bada Umurnin Rufe Makarantun Boko

Jahar Jigawa ta bayar da umurnin rufe makarantun Boko daga yau din nan laraba har zuwa wani lokacin da ba a bayyana ba. Jahohi irin su Kaduna, Kano da Sokoto sun bi sahu. Wannan mataki dai a cewar gwamnatin jahar jigawa na da alaka ne da matsalar ci gaba da yaduwar annobar korona. Amma da dama na ganin hakan bai rasa nasaba da harin da 'yan bindiga suka kai a wata makarantar kimiyya ta kwana da ke Kankarar jahar Katsina ranar jumu'ar da ta gabata ne, in da ake jin sun yi awon gaba da dalibai kusan 500. A jiya kungiyar Boko Haram ta fito ta yi ikirarin daukar alhakin sace yaran, abinda ya jefa tsoro da zullumi a zukatan al'umma.