Skip to main content

Posts

Showing posts from February 4, 2021

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Abduljabbar Nasir Kabara Daga Yin Wa'azi, Ta Rufe Masallacinsa

Malamin nan da aka fi sani da ra'ayi na daban da ke tsaka-tsakin mashabar Shi'a da Darika da ya ke da'awar cewa yake bi. Ya dai hadu da hushin gwamnatin jahar Kano sakamakon kalamansa da gwamnatin ta bayyana da cewa za su iya haddasa fitina a jahar. Abduljabbar Kabara dai sananne ne a kafofin sada zumunta da kuma shafukan YouTube in da ya ke watsa kalamansa da bincike ya tabbatar da sun fi karkata wajen zagin sahabbai, abinda kuma galibin jama'a da malamai suka ce ra'ayi ne irin na Shi'a. Gwamnatin dai ta bakin kwamishinan watsa labaran jahar Muhammad Garba, ta tabbatar da wannan umurnin. Ya kuma kara da cewa an ba kwamishin 'yan sandan jahar umurni da nan take ya tabbatar da an rufe masallacinsa mai suna As-habul Kaf da ke unguwar Gwale, a tsakiyar birnin Kano, tare da bayar da umurnin hana masa duk wani abu da ya kira wa'azi. Sai dai yayin da wannan umurnin ya zo a daren laraba, wasu na ganin batun bai rasa alaka da siyasa, to