Skip to main content

Posts

Showing posts from March 17, 2021

"Ba Zan Taba Sulhu Da 'Yan Ta'adda Ba" - In ji El-Rufa'i

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Tufa'i ya ce ba zai taba yin sulhu da 'yan bindigar da suka sace dalibai 39 a jihar Kaduna ba. Ya ce, "ta yaya za ka dauki kudi ka ba dan ta'addan da zai yi amfani da shi ya sayi makamai wanda zai yi amfani da shi a kan ka". A makon da ya gabata, ‘yan ta’adda sun sace dalibai 39 tare da neman kudin fansa har Naira miliyan 500 daga Gwamnatin Kaduna. Gwamnan ya fada a watan jiya cewa ba zai taba yin sulhu da duk wani dan fashi da makami don neman kudin fansa ba. Jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya na fuskantar yawan sace-sacen mutane, inda makonni biyu da suka gabata wasu mahara suka farma wani rukunin gidajen ma’aikatan Hukumar Filaye Jiragen Sama ta Kasa da ke Kaduna tare da yin awon gaba mutane 11 wanda kawo yanzu ba a san inda suke ba.

"I Will Never Compromise With Terrorists", Says El-Rufai

Kaduna State Governor Malam Nasir El-Tufa'i has said he would never compromise with the gunmen who kidnapped 39 students in Kaduna State. He said, "how can you take money and give it to a terrorist who will use it to buy weapons that will also be used against you". Last week, 39 students were abducted by terrorists and demanded a ransom of 500 million naira from Kaduna State Government. The governor had said last month that he would never reconcile with any armed robber for ransom. The northern Nigerian state of Kaduna has been rocked by a spate of kidnappings in recent weeks, with two weeks ago raiding an airport staff area in Kaduna abducting 11 people and their whereabouts are still unknown.