Skip to main content

Posts

Showing posts from December 10, 2020

Mutum 64 Sun Kamu Da Korona A Kaduna - El-Rufa'i

Gwamnatin jahar Kaduna ta fitar da sanarwar cewa annobar korona ta sake dawowa a jahar. Gwamnatin jahar ta tabbara da samun sabbin kamuwa da cutar har mutum 64, wanda a cewar ta tuni su ma a ka kebe su. An kuma jiyo gwamnan jahar Malam Nasiru El-Rufa'i, na cewa muddin jama'ar jahar suka ci gaba da yin biris da dokokin da aka shata musu to babu makawa gwamnatin za ta sake kulle su ruf har sai lokacin da annobar Covid-19 din ta lafa. Gwamnan ya ce yana mamakin yadda al'umma ke watsi da ka'idojin da tuni aka san da su, na rage cin koso da sanya takunkumi da kuma yawaita wanke hannuwa. Jahar Kaduna na cikin jahohin da suka fuskanci dokar kulle sakamkon barkewar annobar ta korona a watannin baya. To sai dai wannan gargadi na gwamnatin jahar ya gamu da suka, musamman ga wadanda ke kallon kalaman a matsayin na 'yan boko.

Maina Ya Kife A Kotu

 Tsohon shugaban kwamitin hana badakala a hukumar fansho ta kasa Abdulrasheed Maina, ya fadi a kotun birnin tarayya a Abuja, daidai lokacin da ake tsaka da yi masa shari'a. Tsohon shugaban kwamitin dai ana tuhumar sa ne da badakalar da ta danganci batar da kimanin naira biliyan biyu sa'adda da ya ke jagorancin kwamitin. Tun daga lokacin da aka kai shi kotu Maina ya yi batan dabo bayan da ya samu beli. Bayan kwashe tsawon lokaci ana neman sa daga bisa ni an yi nasarar gano shi a kasar Jamhuriyar Nijar. Wannan al'adar faduwa a gaban kwamitocin bincike ba bakuwa ba ce a Najeriya, in da ko watannin baya shugaban kwamitin Hukumar Raya Yankin Naija Delta (NDDC) farfesa Podei ya yi zaman tsumma a kwando, lokacin da yake amsa bahasi a gaban kwamitin majalisar wakilai na kasa dangane da badakalar da ake zargin sa da hannu na karkata kwangiloli da kudaden hukumar zuwa wata hanya daban.