Skip to main content

Posts

Showing posts from May, 2026

Murtala Abdulkadir Dan Iya Ya Ci Gaba da Ƙarfafa Harkokin Ilimi da Haɗin Kan Al'umma a Sokoto

Hukumar Bayar da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen tallafa wa ɗalibai da bunƙasa harkokin ilimi a faɗin jihar, ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Murtala Abdulkadir Dan Iya. Murtala Dan Iya da gwamnan jihar Sokoto Dakta Ahmed Aliyu  Tun bayan hawansa wannan muƙami, hukumar ta mayar da hankali wajen sauƙaƙa wa ɗalibai samun tallafin karatu domin ci gaba da karatunsu a manyan makarantu daban-daban ci da wajen Najeriya. Masu amfani da shirin sun bayyana cewa tallafin na taimakawa wajen rage wa iyaye da ɗalibai nauyin kuɗaɗen karatu da sauran buƙatun makaranta. Gwamnatin Jihar Sokoto ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dakta Ahmed Aliyu ta ci gaba da nuna muhimmanci ga fannin ilimi ta hanyar tallafawa shirye-shiryen da suka shafi ci gaban ɗalibai da inganta harkokin makarantu da samar da kayan aiki da kujeru da tura malaman jami'o'i n jihar waje domin karo karatu, matakin da shugaban hukumar karo ilimin ya dage wajen ganin ya samu nasar...

Turai na fuskantar tsananin zafi

Burtaniya  Wani matsanancin yanayin zafi ya karaɗe yammaci da arewacin Turai, inda yanayin zafi ya zarta yadda aka saba sosai, kuma ya kai yanayin da aka jima ba a gani irinsa ba a ƙasasahe da dama. Birtaniya da Faransa sun fuskanci yanayin zafin da ba su taɓa ganin irinsa ba a watan Mayu, yayin da iska mai huci ta sa zafin ya kai ƙoluwar da ba a saba ganin irinsa ba ko da a lokacin tsanananin zafi.  Paris a Faransa  Jami’an kula da yanayi sun yi gargaɗin cewa yanayin zafin wata alama ce ta ɗumamar duniya.

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya ya shahara wajen ayyukan jinƙai a Jihar Sokoto tsawon  shekarun ya zuwa yanzu. Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto  A tattaunawar da jaridar Tantabara News ta yi da Nura Muhammad Chiso, wanda ke jagorancin daya daga cikin ƙungiyoyin Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya, mai suna da ke bayar da tallafi da wayar da kan al'umma a jihar ta Sokoto, ya bayyana tarin manyan tallafan da wannan shahararren ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya yi wa dubban mutane mabukata a jihar, lamarin da ya ƙara ɗaukaka darajar sunansa a cikin jihar da ma wajenta. N ura Muhammad Chiso  Nura Muhammad Chiso ya ce, "wannan aikin alheri na shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto, wani babban aikin alheri ne da ya gane dubban jama'a talakawa har hakan ya sa suke kiran sa da gambun Sakkwatawa saboda faranta musu rai da yake yi". Ga wa...