Skip to main content

Posts

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Recent posts

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Why are Arab countries worried about the possible collapse of Iran’s government?

After tensions flared between Washington and Tehran following the Iranian government’s brutal crackdown on protesters, Saudi Arabia, Qatar, and Oman launched a major effort to prevent U.S. President Donald Trump from attacking Iran, out of fear that such a move would trigger a “devastating reaction in the region,” a senior Saudi official told AFP. The Saudi official said the three Gulf countries carried out intense diplomatic efforts to persuade the U.S. president to give Iran’s leaders an opportunity to show remorse, adding that communication channels remain open to help build mutual trust. How do the Persian Gulf countries view their “neighbor plagued by instability,” and what are their concerns about its current situation? Gulf diplomacy in a critical moment. The possibility of U.S. military action against Iran has been a key issue causing serious concern in Arab diplomatic efforts, especially among countries of the Gulf region. This concern stems from their proximity to...

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra. Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa. Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta. Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya. Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin. Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba? GA AMSA:  Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da saura...

Sheƙar Tsuntsu Da Ta fi Kowace Girma A Duniya

A kan samu irin wannan sheƙar tsuntsun a ƙasashe kudancin Afirka irin Botswana da Namibiya. Abin mamaki shi ne wani ɗan ƙaramin tsuntsu ne mai suna Philetairus socius kan yi wannan sheƙa .   Ta yi kama da saƙar zuma, kuma ya kan nemi bishiyoyi masu ƙarfi kamar gawo da bagaruwa da farar ƙaya sannan ya yi wannan sheƙa. Ta kan jure ruwan sama da zafin rana har ma da tsananin sanyin hunturu. A cikin sheƙa ɗaya akan samu ɗakuna kamar ɗari, ƙofofin kusa da juna. Masu nazarin rayuwar tsuntsaye na ganin wannan tsuntsu shi ne irin sa na farko a duniya ɗan ƙarami da kan gina sheƙa mai girma kamar wannan. Faɗin sheƙar ya kan iya kai har ƙafa 20 tsawonta kuma ƙafa 10. 

Barista Yunusa Ari Ya Yi Ɓatan Dabo

Dakataccen kwamishin hukumar zaɓe na jahar Adamawa, Barista Yunusa Hudu Ari, ya ranta cikin na kare jim kaɗan bayan da shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya nemi a gudanar da cikakken bincike game da badaƙalar da ake zargin sa da ita. Kakakin hukumar INEC Festus Okoye ne ya sanar da gidan talabijin na Channels haka. Okoye ya ce su kansu ba za su iya cewa ina ya shiga ba saboda tun bayan faruwar lamarin ba ya ɗaukar kiran waya kuma sun ma daina jin ɗuriyarsa gaba ɗaya. Da aka tambai shi ko akwai wani mataki da hukumar INEC za ta ɗauka kan wannan sabon lamari, sai ya ce, "ai wannan hakkin jami'an tsaron 'yan sanda ne na tabbatar da sun san inda yake. Idan har jami'an tsaro na buƙatar gurfanar da shi, su ne za su iya zaƙulo shi tare da gabatar da shi a gaban shari'a". Hudu Ari dai ya sanar da sakamakon zaɓen gwamnan jahar Adamawa a ranar Lahadin makon jiya, inda ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen tun gabanin a kammala tat...

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Tsaunin Hin Sam Wan Mai Ɗimbin Shekaru A Duniya

Tsaunukan Hin Sam Wan , da kuma aka fi sani da Dutsen Whale Uku, wasu tsaunuka ne ma su ban sha'awa da suka kai kimanin shekaru miliyan 75.  Suna cikin daga tsaunukan ƙasar Thailand masu ban mamaki.  Sunansu ya samo asali ne daga kamanninsa, idan aka dubi tsaunin daga sama daga sama za a ga ya yi kama da dangin whales wato dabbar nan ta tekun mai kama da kifi whale.

Putin Ya Ziyarci Sansanin Soja Na Kherson Da Ke Ukraine

Shugaban Rasha Vladimir Putin ya ziyarci yankunan Ukraine da aka mamaye a karo na biyu tun bayan ƙaddamar da wani gagarumin farmaki, kamar yadda fada Kremlin ta sanar a yau Talata. Putin ya ziyarci hedkwatar soji a yankin Kherson na kudancin ƙasar Ukraine da kuma hedkwatar tsaron Rasha da ke yankin Luhansk. Tafiyar ta zo ne a daidai lokacin da Rasha ke ci gaba da kai hare-hare a gabashin Ukraine. Jaridar ƙasar Rasha ta The Moscow Times   https://www.themoscowtimes.com/2023/04/18/putin-visits-occupied-ukraine-territories-a80862 ta bayyana cewa Fadar Kremlin ba ta bayyana takamaiman lokacin da tafiyar ta gudana ba kuma hotunan ziyarar biyu sun nuna Putin sanye da tufafi daban-daban.