Skip to main content

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra.
Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa.
Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta.
Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya.

Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin.
Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba?

GA AMSA: 

Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da sauran jama'a su lura da musabbabin haɗarin idan na mota ne, ko jiragen ruwa (kamar kwale-kwale) da sauran su. Wannan zai sa a ji shin 'min indilLahi' ne ko kuwa an yi halin Ɗan Adam na ɗora kaya fiye da kima?
Kenan ba labarin ne kawai muke bayarwa kara-zube ba, muna da wani horo na musamman a ƙarƙashin bayar da labarin shi kansa.
Misali, a lokutan hunturu ya zama wajibi a yi nesa da duk wani makamashi irin asaha da ƙyastu da man fetur da ma kananzir, musamman ga yara. Baya ga faɗakarwa, hasalima akwai sanar da damuwar waɗanda lamarin ya shafa ga masu iya taimaka mu su.
Da ba mu bayar da labari irin na yaƙi da yunwa, da fari da kuwa Majalisar Ɗunkin Duniya har ma da hukumomin bayar da agaji ba su kai agajin gaggawa na kayan abinci da ruwan sha ga waɗannan jama'a ba. Da ba mu bayar da labari irin na ambaliyar ruwa da kifewar kwale-kwale da ɓarkewar annoba da curutoci irin na maleriya waɗanda hukumomin bayar da agaji irin NEMA da na NCDC, masu dakile cutuka masu yaɗuwa ba su san da shi ba to ina kuwa ga ɗaukar mataki!
2. A rukuni na biyu, matsayina na ɗan jarida, na kan saka ido game da lamurran da ke cikin jama'a da zamantakewarsu da muhalli da kewayensa da shuwagabannin talakawa na gargajiya da 'yan siyasa. 

Kullum rana kuwa zan nemi labarin tafiyar lamurra. An ɗora min alhakin zama ido da kunnuwan jama'a; in kuma zama bakinsu in da ba su iya magana. Kafin in ɗora alhakin zubar da shara barkatai kan gwamnati a lokaci guda, sai na lura su kansu mutane wace rawa suke takawa wajen tsaftace muhalli. Wato kenan idan Laila ta ƙi sai a koma Basha!
Idan annobar gudu da amai ta ɓarke a ƙauyuka da sassan birane, muddin zan haɗa rahoto, dole ne in saurari kowane ɓangare. Baya ga alhakin gwamnati na samar da magani, akwai kuma tsaftace ruwan sha. Baya ga kawo ma al'umma agaji, akwai kuma wayar mu su da kai na yadda za su lazimci tsaftar ruwa da kare kai. Wannan kenan sai na bi ta kan kowa: gwamnati, don sanin shin ta kai agaji da gaggawa, idan maleriya ce sun raba ragar sauro kan lokaci, ko suna bayar da magungunan da juddum hukumomin lafiya ke bayar da tallafi?
Su kuma jami'an kiyon lafiya na aikinsu wajen amfani da kafafen watsa kabari da taruka wajen wayar da kan jama'a tare da taimakon hukumomin lafiya ko kuwa su ma al'ummar gari. Sakamakon da zai fito shi ma zai zama abin misali ga wasu.

3. Rukuni na uku, shi ne na masu mulkin talakawa. Cikin su akwai masu yin ayyukan da talaka ya ɗora mu su, akwai kuma ma su watsi da wannan hakki. Idan gwamnati ta ƙaddamar da rabon kayan amfanin gona misali taki da garmar shanu da irin shuka da magungunan ƙwari ga manoma. Har ma aka gayyaci 'yan jarida domin su shaida.
Matsayina a nan shi in zama wakilin talaka, idonsa da kunnuwa da kuma bakinsa.
Shin mai karatu ka san irin labarin da nake nema a nan?
Idan ba ka sani ba to ga amsa:

A irin wannan yanayi, zan nemi labarin da zai amfani mai gaskiya tsakanin mahukunta da talakawansu. 

A irin wannan lamari, babban abin mayar da hankali shi ne:

1. Su wa aka zaɓa domin ba su tallafin, kuma saboda me aka zaɓe su?
2. Akwai waɗanda aka hanawa tallafin, kuma saboda me?

3. An saka siyasa a ciki?

4. A wane lokacin shekara aka bayar da tallafin (misali, farkon damina ne ko bayan an girbe amfanin gona, ko kuwa lokutan zaɓe ne?)

5. Sannan waɗanne irin jawabai gwamnati ta yi da za su sa in fahimci manufar bayar da tallafi.

6. Su waye suka nuna murna kuma su waye suka nuna rashin gamsuwa (misali, na su nuna damuwa 'yan adawa ne ko wake da shinkafa ne?)

To a nan ne fa wasu za su ce muna wallafa "negative stories" wato labaran da ba su da daɗi ga wasu mutane.

Zan mayar da hankalina ga ma su ƙorafi. In ji me ya sa su ke ƙorafin!
Su ne za su taimaka ma zaren labarina in bi shi tiryan-tiryan har sai na gano gaskiya. Zan yi amfani da muryoyinsu (idan sun amince da haka, idan kuma suna da shakku ga abinda zai faru da su, zan tabbatar da na ɓoye sirrinsu da kuma asalin inda na samo labarina).

Zan tunkari masu gari domin ji daga ɓangarensu. A wurin mahukunta wannan shi ne labari maras daɗin ji, musamman idan akwai badakalar cin hanci a cikin bayar da tallafin.
Zan nemi sanin dalilin ware wasu a bisa siyasa ko addini ko ƙabilanci. Zan nemi sanin dalilin da ya sa wasu suka yi ma gwamnati yarfe domin kawai adawar siyasa. Zan zama tsakiya da zimmar tabbatar da gaskiyar lamari, in fitar da kome a zahiri inda hakan zai kawar da zargi da kuma kare kaina.
Lallai ne duk labarin yabo da tallata wani ko wasu in guje shi domin ba shi ne aikina ba! Abinda nake nema shi ne, shin an yi ma talaka adalci ko an murkushe shi, ta haka zan san yadda zan fallasa badaƙalar.
To irin wannan ne wasu ke kira labari maras daɗin ji, negative story, wai daga an mutu sai an lalace.
ZUABIRU AHMAD BASHIR,ƊAN JARIDA NE A RADIYO NAJERIYA (FRCN).
MAI NEMAN TUNTUƁA TA:


Comments

Wadanda aka fi karantawa

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Wata Mota Cike Da Harsasan Bindiga Ta Fada Rami A Garin Awka Na Jahar Imo

Hankalin jama'a yayi matukar tashi a jiya Lahadi biyo bayan gano wata babbar mota cike da harsasai masu rai a birnin Anacha na jahar Imo da ke kudu maso gabashin tarayyar Najeriya. Rahotannin da suka shigo muna na cewa jami'an tsaron cikin hanzari sun afkawa garin na kasuwanci domin daukar matakin gaggawa kan lamarin.  Babbar motar wadda ke dauke da kwaliyoyin harsasai masu rai ta fada cikin wani rami da ke kan titi, inda dukan harsasan suka zube. Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce: “Motar ta fadi, kuma duk titin na cike da harsasai.  Wasu yaran ma sun debi wasu da hannayensu suka gudu, kafin jami’an tsaro su iso wurin. ”  Majiyar ta ci gaba da bayyana cewa direban babbar motar da mai yi masa hidima sun yi watsi da motar bayan hatsarin ya faru, inda suka yi batan dabo zuwa inda ba a sani ba. Amma wata majiyar ta ce ‘yan sanda sun cafke direban. “Lamarin ya jawo jami'an tsaro masu yawa zuwa yankin hanyar Awka da da safiyar yau. 'Yan sanda sun...

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

An Ruguza Makarantar Malam Abduljabbar Kano

Dazu dazun nan gwamnatin jahar Kanon ta tura jami'an ma'aikatar lura da tsarin filaye in da ta ruguza makarantar Malam Abduljabbar. Gwamnatin dai ta taba bayyana cewa filin da ya ke amfani da shi haramtacce ne, in da ta kai ga kwace shi tare da bada umurnin gudanar da wasu muhimman ayukka a wurin. Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin gwamnatin jahar Kano da Abduljabbar in da a ranar laraba sakataren watsa labaran gwamnatin jahar, Muhammad Garba ya bayar da sanarwar rufe masallacin Malam Abduljabbar tare da hana masa gudanar da wa'azi baki daya. In da ta ce hakan na da alaka da irin yadda ya ke tunzura jama'a a kalaman da ya ke amfani da su a lokacin da ya ke da'awa.

Gunmen Abducted 11 FAAN Staff In Kaduna

A group of gunmen yesterday attacked the residences of the Federal Airport Authority of Nigeria Kaduna. Reports say gunmen stormed the compound and abducted at least 11 people. Recent reports suggest that the bandits also abducted a staff of  Nigerian Airspace Management Agency NAMA, his wife, a National Meteorological Agency (NIMET) official and his children.Their whereabouts are still unknown. Kidnappings are common in Nigeria today, and almost every morning there are reports of killings or kidnappings for ransom. Last week Nigerian President Muhammadu Buhari vowed to end abduction in Nigeria but for all indications his words were not effective.

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."

Burtaniya Ta Kakabawa Bankunan Rasha da Mahukuntan Kasar Takunkumin Tattalin Arziki Mafi Girma A Tarihi

Getty images Firaministan Burtaniya, Boris Johnson ya sanar da sakawa Rasha takunkumi mafi tsanani a bangaren tattalin arziki da Rasha ta taba gani, tun bayan da ta mamaye Ukraine. Da yake magana a zauren majalisar, firaministan ya ce za a daskarar da duk wasu manyan bankunan kasar Rasha da kuma cire su daga tsarin kudi na Burtaniya.  Har ila yau, za a dakatar da kamfanin jiragen saman Rasha na Aeroflot sauka a kasar Birtaniya. Mista Johnson ya shaidawa majalisar dokokin kasar a yammacin ranar almais din makon nan cewa, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin "mai cin zali ne mai zubar da jini, don haka zai yabawa aya zakinta".

Yahaya Bello Ya Caccaki Buhari

Da ya ke jawabi a lokacin da ake gudanar da shirin zaben fitar da gwani, gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello ya nemi a zabe shi domin ya magance matsalar tsaro da karancin ilmi da ake fama da su yanzu haka a Najeriya. Ya ce, "akwai takaici ace wai yanzu malaman jami'a suna ci gaba da yajin aiki, dalibai na zaune a gida kuma an kasa magance wannan matsala mai saukin magancewa". Yahaya Bello wanda ya ce ba zai jaye ma kowa a neman tikitin shugaban kasa, ya kara da cewa shi matashi ne kuma matasa ya kamata a ba dama su mulki kasar nan ba tsofaffi da suka gaji ba. Ya yabawa shugaba Buhari akan saka hannu a kan dokar ba matasa damar tsayawa takara, in da ya ce abu ne mai kyau. Ya yi kira ga mata da sauran 'yan Najeriya da ya ce ana zalunta da su zabe shi. Dan takarar ya ce "yanzu haka babu tsaro ko kadan kuma an kyale, ana kashe mutane ana kona mu su dukiya kuma ana kallo an zura ido".

Binani Ta Zama Mace Ta Farko Da AKa Zaɓa Gwamna A Najeriya

A wani abinda ba saban ba, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Sanata Aisha Dahiru, wacce aka fi sani da Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen gwamnan jahar Adamawa. Kwamishinan zaɓen jahar Adamawa, Farfesa Hudu Yunus Ari, ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ana tsakiyar tattara sakamakon zaɓen. An bayyana sakamako daga ƙananan hukumomi 10 cikin 20 yayin da aka dage ci gaba da bayyana sakamakon zaɓen har zuwa karfe 11 na safe. Sai dai Ari ya sanar da sakamakon ƙarshe awa ɗaya kafin lokacin da aka tsara. Gwamnan jahar Ahmadu Fintiri na jam'iyyar PDP ne ke kan gaba kafin a bayyana hakan. Wasu magoya bayan jam’iyyar PDP a zauren sun nuna rashin amincewarsu da dalilin da ya sa kwamishinan zaɓe ya sanar da sakamakon maimakon baturen tattara sakamakon zaɓe a al'adance.