Skip to main content

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra.
Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa.
Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta.
Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya.

Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin.
Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba?

GA AMSA: 

Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da sauran jama'a su lura da musabbabin haɗarin idan na mota ne, ko jiragen ruwa (kamar kwale-kwale) da sauran su. Wannan zai sa a ji shin 'min indilLahi' ne ko kuwa an yi halin Ɗan Adam na ɗora kaya fiye da kima?
Kenan ba labarin ne kawai muke bayarwa kara-zube ba, muna da wani horo na musamman a ƙarƙashin bayar da labarin shi kansa.
Misali, a lokutan hunturu ya zama wajibi a yi nesa da duk wani makamashi irin asaha da ƙyastu da man fetur da ma kananzir, musamman ga yara. Baya ga faɗakarwa, hasalima akwai sanar da damuwar waɗanda lamarin ya shafa ga masu iya taimaka mu su.
Da ba mu bayar da labari irin na yaƙi da yunwa, da fari da kuwa Majalisar Ɗunkin Duniya har ma da hukumomin bayar da agaji ba su kai agajin gaggawa na kayan abinci da ruwan sha ga waɗannan jama'a ba. Da ba mu bayar da labari irin na ambaliyar ruwa da kifewar kwale-kwale da ɓarkewar annoba da curutoci irin na maleriya waɗanda hukumomin bayar da agaji irin NEMA da na NCDC, masu dakile cutuka masu yaɗuwa ba su san da shi ba to ina kuwa ga ɗaukar mataki!
2. A rukuni na biyu, matsayina na ɗan jarida, na kan saka ido game da lamurran da ke cikin jama'a da zamantakewarsu da muhalli da kewayensa da shuwagabannin talakawa na gargajiya da 'yan siyasa. 

Kullum rana kuwa zan nemi labarin tafiyar lamurra. An ɗora min alhakin zama ido da kunnuwan jama'a; in kuma zama bakinsu in da ba su iya magana. Kafin in ɗora alhakin zubar da shara barkatai kan gwamnati a lokaci guda, sai na lura su kansu mutane wace rawa suke takawa wajen tsaftace muhalli. Wato kenan idan Laila ta ƙi sai a koma Basha!
Idan annobar gudu da amai ta ɓarke a ƙauyuka da sassan birane, muddin zan haɗa rahoto, dole ne in saurari kowane ɓangare. Baya ga alhakin gwamnati na samar da magani, akwai kuma tsaftace ruwan sha. Baya ga kawo ma al'umma agaji, akwai kuma wayar mu su da kai na yadda za su lazimci tsaftar ruwa da kare kai. Wannan kenan sai na bi ta kan kowa: gwamnati, don sanin shin ta kai agaji da gaggawa, idan maleriya ce sun raba ragar sauro kan lokaci, ko suna bayar da magungunan da juddum hukumomin lafiya ke bayar da tallafi?
Su kuma jami'an kiyon lafiya na aikinsu wajen amfani da kafafen watsa kabari da taruka wajen wayar da kan jama'a tare da taimakon hukumomin lafiya ko kuwa su ma al'ummar gari. Sakamakon da zai fito shi ma zai zama abin misali ga wasu.

3. Rukuni na uku, shi ne na masu mulkin talakawa. Cikin su akwai masu yin ayyukan da talaka ya ɗora mu su, akwai kuma ma su watsi da wannan hakki. Idan gwamnati ta ƙaddamar da rabon kayan amfanin gona misali taki da garmar shanu da irin shuka da magungunan ƙwari ga manoma. Har ma aka gayyaci 'yan jarida domin su shaida.
Matsayina a nan shi in zama wakilin talaka, idonsa da kunnuwa da kuma bakinsa.
Shin mai karatu ka san irin labarin da nake nema a nan?
Idan ba ka sani ba to ga amsa:

A irin wannan yanayi, zan nemi labarin da zai amfani mai gaskiya tsakanin mahukunta da talakawansu. 

A irin wannan lamari, babban abin mayar da hankali shi ne:

1. Su wa aka zaɓa domin ba su tallafin, kuma saboda me aka zaɓe su?
2. Akwai waɗanda aka hanawa tallafin, kuma saboda me?

3. An saka siyasa a ciki?

4. A wane lokacin shekara aka bayar da tallafin (misali, farkon damina ne ko bayan an girbe amfanin gona, ko kuwa lokutan zaɓe ne?)

5. Sannan waɗanne irin jawabai gwamnati ta yi da za su sa in fahimci manufar bayar da tallafi.

6. Su waye suka nuna murna kuma su waye suka nuna rashin gamsuwa (misali, na su nuna damuwa 'yan adawa ne ko wake da shinkafa ne?)

To a nan ne fa wasu za su ce muna wallafa "negative stories" wato labaran da ba su da daɗi ga wasu mutane.

Zan mayar da hankalina ga ma su ƙorafi. In ji me ya sa su ke ƙorafin!
Su ne za su taimaka ma zaren labarina in bi shi tiryan-tiryan har sai na gano gaskiya. Zan yi amfani da muryoyinsu (idan sun amince da haka, idan kuma suna da shakku ga abinda zai faru da su, zan tabbatar da na ɓoye sirrinsu da kuma asalin inda na samo labarina).

Zan tunkari masu gari domin ji daga ɓangarensu. A wurin mahukunta wannan shi ne labari maras daɗin ji, musamman idan akwai badakalar cin hanci a cikin bayar da tallafin.
Zan nemi sanin dalilin ware wasu a bisa siyasa ko addini ko ƙabilanci. Zan nemi sanin dalilin da ya sa wasu suka yi ma gwamnati yarfe domin kawai adawar siyasa. Zan zama tsakiya da zimmar tabbatar da gaskiyar lamari, in fitar da kome a zahiri inda hakan zai kawar da zargi da kuma kare kaina.
Lallai ne duk labarin yabo da tallata wani ko wasu in guje shi domin ba shi ne aikina ba! Abinda nake nema shi ne, shin an yi ma talaka adalci ko an murkushe shi, ta haka zan san yadda zan fallasa badaƙalar.
To irin wannan ne wasu ke kira labari maras daɗin ji, negative story, wai daga an mutu sai an lalace.
ZUABIRU AHMAD BASHIR,ƊAN JARIDA NE A RADIYO NAJERIYA (FRCN).
MAI NEMAN TUNTUƁA TA:


Comments

Wadanda aka fi karantawa

Breaking: Chadian President Idris Deby Is Dead

  Chadian President Idris Deby died while leading the country's security forces over the weekend, fighting rebels on the northern country's border with Libya.  President Deby is widely expected to win the country's general election by 80 percent after seeking a sixth term.  The military has dissolved parliament and announced that it would hold power for 18 months before new elections.  Idris Deby took power in Chad in 1990 after overthrowing the government of former President Hissene Habry, and has ruled Chad for 30 years.

Stepping Down Not The Right Option - Osinbajo

Vice president Yemi Osinbajo has denied reports that he intends to step down for a certain presidential aspirant ahead of the presidential primary of the All Progressives Congress (APC). The denial is contained in a statement by the chairman of Osinbajo’s campaign council, Richard Akinnola on Sunday. According to the statement, the people behind the speculation are “afraid of the huge political support base of the Vice President, Prof. Yemi Osinbajo,” adding that the VP is ready for the presidential primary scheduled to hold between June 6 and 8. The campaign council “welcomes our distinguished delegates from across the country to Abuja for our presidential primaries. “As you settle down in Abuja, we implore you to kindly disregard various fake news making the rounds that Prof. Yemi Osinbajo has stepped down. “Osinbajo would be hoping to clinch the ticket of the ruling party with much desire to take over from his principal, President Muhammadu Buhari at the end of his tenur...

'Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidajen Ma'aikatan Filayen Jiragen Saman Najeria Tare Da Sace Mutum 11

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari a gidajen ma'aikatan Hukumar Filin Jirgin Saman Tarayyar Najeriya da ke Kaduna, inda suka yi awon gaba da akalla mutane 11. Rahotannin baya-bayan nan sun kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi nasarar sace ma’aikacin Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NAMA)A, da matarsa, da jami’in Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NIMET) da ya’yansa, kuma har yanzu ba a san inda suke ba. Satar mutane ya zama ruwan dare a Najeriya a yau, kuma kusan kowace safiya ana samun rahotannin kashe-kashe ko satar mutane don neman kudin fansa.  A makon da ya gabata ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin kawo karshen satar mutane a Najeriya amma ga dukkan alamu kalaman nasa ba su yi tasiri ba. 

PDP Na Shirin Korar Wike

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya shigar da ƙara domin hana wani sabon yunƙurin jam’iyyar PDP dakatar da shi daga cikinta, kuma ya buƙaci kotun da ta ɗauki mataki ga duk masu wannan aniya.  Ɗaya daga cikin jigajigan jam'iyyar PDP da suka mayar da martani kan ƙarar da gwamna Wike ya shigar, Mahdi Shehu, ya mayar da martani a ranar Litinin da ta gabata inda ya wallafa a shafinsa na twitter wata sanarwa cewa, “Wike ya shigar da ƙara kan jam’iyyar PDP mai lamba FHC/ABJ/CS/139/2023 ta hannun lauyoyinsa, DY Musa (SAN);  Douglas Moru, da C. C. Chibuike, yana neman a ba shi umarnin hana a kore shi daga PDP.”   Wike dai ya yi ta famar ruguza jam’iyyar har ma ya rasa inda za shi. Gwamnan na Ribas ya zamewa jam'iyyar PDP ƙadangaren bakin tulu, irin yadda ya ke uwa da makarbiya tun bayan da dangantaka ta soma tsami tsakaninsa da wasu jigajigan jam'iyyar ciki kuwa har da gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.  

Farkawar Matan Afirka

Afirka nahiya ce mai dogon tarihi. Tun asali,  yawancin Turawa sun yi kokarin sanya idanu a kan nahiyar, sun ziyarce ta don neman ko dai kasuwanci, wanda a wancan lokacin wani nau'i ne na cinikin bayi ko kuma daga baya ya koma ga cinikin kayan masarufi kamar su gyada, auduga, fatun dabbobi da makamantansu. Zuwan Larabawa kuma, a wasu lardunan Afirka na lokacin, gami da yankin da ake kira "Sudaniyya", wanda ya hada da Sudan, Najeriya, Chadi, da wasu sassan Jamhuriyar Nijar, ya haifar da yaduwar Musulunci da al'adun Gabas. Daga baya, zuwan Bature ya kawo kiristanci, ilimin yamma da sauran manufofin Turawa. Nahiyar Afirka sannu a hankali tana juyawa zuwa matakai daban-daban; daga duhun kai har zuwa halin da ake ciki a yau. Ilimin addini da na zamani sun samu gindin zama a kasashen Afirka, amma har yanzu mata suna baya a wannan tafiyar. Sau da yawa za ka ga mata a yankunan karkara har ma da wasu biranen Afirka ci...

Filin Jiragen Sama Na Malam Aminu Kano Zai Ci Naira Biliyan 700

Ministan suhurin jiragen sama Alhaji Hadi Sirika, ya bayyana cewa majalisar zartaswata ƙasa ta amince da ware fiye da naira biliyan ɗari bakwai domin aikin kwangilar gyaran filin sauka da tashin jiragen na sama na duniya na Malam Aminu Kano, wanda ya ce za kammala a cikin shekara ɗaya rak. Majalisar zartaswa ta ƙasa ta kuma amince da ware naira biliyan ɗari da goma sha bakwai domin gudanar da kwangilar gina cibiyar bincike akan man fetur ta Oloibir a yankin Naija Delta. Ministan ƙasa a ma’aikatar albarkatun man fetur, Timipre Sylva ne ya shaidawa ‘yan jaridar fadar shugaban ƙasa hakan, inda ya ce za a kammala aikin kwangilar a cikin shekaru biyu da rabi. Ya ce tun a 1980 gwamnatin Alhaji Shehu Aliyu Shagari ta soma aikin, amma daga bisani aka yi watsi da shi wanda a yanzu zai zama ɗaya daga cikin manyan ayyukan da za a ci ga da tunawa da shugaba Muhammadu Buhari a yankin Naija Delta mai arzikin man fetur.

Dalar Amurka Na Fuskantar Barazanar Durkushewa

Shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya soki kasar Amurka akan irin rawar da dala ke takawa a tattalin arzikin duniya tare da yin kakkausar suka ga asusun lamuni na duniya na IMF. Lula ya yi waɗannan kalamai a wata ziyarar aiki da ya kai Chana, jiya Alhamis a birnin Shanghai a wani bikin kaddamar da takwaransa, Dilma Rousseff a matsayin sabuwar shugabar bankin raya kasashen BRICS, da gamayyar kasashenn Brazil da Rasha da Indiya da Chana da kuma Afirka ta Kudu suka samar. "Me ya sa kowace ƙasa za a danganta da dala don kasuwanci? Wanene ya yanke shawarar dala za ta zama kuɗin duniya?"  Ya ƙara da cewa me yasa banki kamar bankin BRICS ba zai iya samun kuɗin da zai gudanar da hulɗar kasuwanci tsakanin Brazil da Chana ba, da ma sauran ƙasashen duniya? Ya ce yana mamakin yadda ƙasashe cike da rauni  su ke bin sawun amfani da dala wajen gudanar da kasuwanci alhali suna iya hakan da kuɗaɗensu. A wata ganawa tsakanin sa da shugaban Chana Xi Jinping, da kuma ya ...

Nigerian President Vaccinated Against Covid-19

Nigerian President Muhammadu Buhari and his vice president, Professor Yemi Osinbajo, have been vaccinated with AstraZeneca vaccine, just one day after the nationwide vaccination campaign. Earlier, the Federal Government announced that as soon as the vaccine arrives in Nigeria, the President, government officials and all Governors will be at the forefront of the immunization drive which would be shown on the National Television (NTA) to set an example for other Nigerians, as well as allay their fears about the legitimacy of the vaccine. The president's doctor, Dr. Shuaibu Rafindadi, vaccinated the president at 11:53 a.m. Nigerian time (10:53 a.m. GMT) on Saturday, and Vice President Yemi Osinbajo immediately joined the process. They were also provided with electronic immunization cards by the Director General of Primary Health Care Development (NPHCDA), Dr. Faisal Shuaib. Nigeria successfully started the vaccination on Tuesday, becoming the third West African country to ...

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Israel Targets Journalists

GAZA: An Israeli airstrike destroyed a high-rise building in Gaza City that housed offices of The Associated Press and other media outlets on Saturday, the latest step by the military to silence reporting from the territory amid its battle with the militant group Hamas. The strike came nearly an hour after the military ordered people to evacuate the building, which also housed Al-Jazeera, other offices and residential apartments. The strike brought the entire 12-story building down, collapsing with a gigantic cloud of dust. There was no immediate explanation for why it was attacked. The strike came hours after another Israeli air raid on a densely populated refugee camp in Gaza City killed at least 10 Palestinians from an extended family, mostly children, in the deadliest single strike of the current conflict. Both sides pressed for an advantage as cease-fire efforts gathered strength. The latest outburst of violence began in Jerusalem and has spread across the region, with...