Skip to main content

Posts

Showing posts from August 2, 2022

Kalubalen Tsaro Da Canza Shekar Kwamishinan Tsaron Jahar Sokoto

  A daidai lokacin da matsalar tsaro ke ʙ ara taā€™azzara a jahar Sokoto, kwamishinan tsaron jahar Kanal Garba Moyi (mai ritaya) ya bayar da sanarwar aje mu ʙ aminsa tare da ficewa daga jamā€™iyyar jamā€™iyar PDP mai mulkin jahar. A cewar tsohon kwamishinan tsaron, ā€œakwai gaggan matsaloli da suka taka rawa wajen ficewarsa daga jamā€™iyayar, da suka ha ɗ a da sakacin gwamnan jahar, Aminu Waziri Tambuwal na watsi da dukan   shawarwarin da ake ba shi da suka shafi tsaro; kazalika da rashin sauraren ʙ orafe- ʙ orafen dangane da ci gaban jahar a fannoni da damaā€. A ranar alhamis da ta gabata dai wasu ā€˜yan bindiga suka kai wani hari a garin Chakai da ke ʘ aramar Hukumar Mulki ta Tambuwal, wadda ita ce mahaifar gwamnan jahar, in da suka sace mutum goma sha bakwai ciki har da mata da ʙ ananan yara, tare da neman diyyar naira miliyan takwas da dubu ɗ ari biyar. Kazalika, sun fitar da sanarwar shirin hallaka mutanen daga gobe talata, muddin ā€˜yan uwan wadanda ake garkuwa da sun ba su aika...