A daidai lokacin da matsalar tsaro ke Ę ara taāazzara a jahar Sokoto, kwamishinan tsaron jahar Kanal Garba Moyi (mai ritaya) ya bayar da sanarwar aje mu Ę aminsa tare da ficewa daga jamāiyyar jamāiyar PDP mai mulkin jahar. A cewar tsohon kwamishinan tsaron, āakwai gaggan matsaloli da suka taka rawa wajen ficewarsa daga jamāiyayar, da suka ha É a da sakacin gwamnan jahar, Aminu Waziri Tambuwal na watsi da dukan shawarwarin da ake ba shi da suka shafi tsaro; kazalika da rashin sauraren Ę orafe- Ę orafen dangane da ci gaban jahar a fannoni da damaā. A ranar alhamis da ta gabata dai wasu āyan bindiga suka kai wani hari a garin Chakai da ke Ę aramar Hukumar Mulki ta Tambuwal, wadda ita ce mahaifar gwamnan jahar, in da suka sace mutum goma sha bakwai ciki har da mata da Ę ananan yara, tare da neman diyyar naira miliyan takwas da dubu É ari biyar. Kazalika, sun fitar da sanarwar shirin hallaka mutanen daga gobe talata, muddin āyan uwan wadanda ake garkuwa da sun ba su aika...