Skip to main content

Posts

Showing posts from February, 2023

Tinubu Na Gaban Tambuwal A Sokoto

Asiwaju Bola Tinubu, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, ya ba Atiku Abubakar, ɗan takarar jam’iyyar PDP a jihar Sokoto rata a jahar.   Duk da cewa akwai kananan hukumomi 23 a jihar, Tinubu ya tattara mafi yawan kuri’u a kananan hukumomi 10. Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya samu kuri’u 101,608, Alhaji Atiku Abubakar ya samu kuri’u 98,080 yayin da Sanata Rabi’u Kwankwaso na jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP) ya zo na uku da kuri’u 314 sannan Peter Obi na jam’iyyar Labour ya samu kuri’u 171. Kananan Hukumomin Da Aka Samu Sakamakonsu TURETA  Waɗanda aka yi ma rajita: 40,746  Waɗanda aka tantance: 16,516  APC 7, 684  LP.  1  NNPP.  9  PDP.  8, 144  KWARE  Waɗanda aka yi ma rajita 74,056  Waɗanda aka tantance 24,776  APC 10,485  LP.  63  NNPP.  11  PDP.  12,242  BODINGA  Waɗanda aka yi ma rajita 86,139  Waɗanda aka tantance 28,054  A 1  AA0 ku  AAC.  9  ADC.  21  ADB.  93  APC 13,384  APGA 26  APM.  7  APP 5  BP.  1  LP.  10  NNPP.  39  NRM.  33  PDP.  13,559  PRP  1

Sakamakon Zaɓen Shugaban Ƙasa Kai Tsaye

Za mu ci gaba da kawo muku sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisar dokoki na ƙasa. Hoto: BBC Hausa

An Kashe Ɗan Takarar Jam'iyyar Labour A Kudu Maso Gabas

Ana ci gaba da samun tashe-tashen hankula a yankin Kudu maso Gabas hatta a cikin makon da za a gudanar da babban zaɓen 2023. Rahotanni daga yankin sun ce wasu da ba gano ba sun kashe Mista Oyibo Chukwu, ɗan takarar ɗan majalisar dattawa mazabar Enugu ta gabas a ranar Asabar, sa’o’i 48 kafin gudanar da zaɓen. An kashe Chukwu ne tare da wasu magoya bayansa biyar a ƙaramar hukumar Awkunanaw ta Enugu a lokacin da yake dawowa daga wani gangamin yaƙin neman zaɓe. An kuma ce masu kisan sun kona shi da magoya bayansa bayan sun tare da shi a cikin motarsa. Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar Labour, Chijioke Edeoga, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce jam’iyyun siyasa na yi wa ‘ya’yan jam’iyyarsa kisan gilla, waɗanda ke ganin barazana ce ga bunƙasar jam’iyyar a jihar. Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour, ya fito ne daga yankin Kudu maso Gabas, wanda tashin hankali ya zama ruwan dare, tun kafin lokacin zaɓe.  Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sha alwashin

Tsakanin Kyanwa Da Ɓeraye...

Mage ta zauna ta yi jugum ta rasa abinda ke yi mata daɗi, ko ina sai karɓar saƙon zagi da suka take yi daga dabbobin dawa da suka kiwata ta da guminsu saboda yaƙi da ɓeraye. An zargi Mage da ba wa ɓeraye damar sace daddawar jamhuriya ba tare da ɗaukar mataki ba. Ga shi kuma wa'adin mulkin Mage ya ƙare dole ta koma gefe ta zama ƴar kallo. Shin ko me Mage zata yi don kawo ƙarshen ɓarnar ɓeraye da suka tara daddawar jamhuriya don gadar kujerar Mage? Mage ta fesa fiya-fiya akan wannan daddawar miya, wanda yanzu haka ƙwari da ɓeraye suka gano Mage ta shirya ganin bayan su don haka suka haɗa kai domin yaƙar ta. A baya kowane ɓera mai riƙe da ragamar mulki ya ci karensa ba babbaka. Ya yi mulkin mallaka da kama karya. Ya saci daddawar miya son ransa, ya yaƙi duk wanda ya ɗaga masa murya, ya halatta kansa rusa akurkin kaji ba bisa ƙa'ida ba, ya mallake shingayen ƙananan dabbobi ba bisa ƙa'ida ba. Duk da babbar majalisar dokokin zartaswa ta hana su ba su yarda ba, amma a

DA DUMI DUMI: CBN Ya Ce Kada Bankuna Su Amshi Tsofaffin Kuɗi

'Yan sa'o'i da fitar da Babban Bankin Najeriya CBN ya fitar da sanarwar cewa bankuna na iya amsar tsofaffin takardun kuɗin naira 500 da naira 1000 daga hannun jama'a, to sai dai Bankin na CBN ya yi amai ya lashe in da ya ce bai amince bankuna su amshi takardun kuɗin naira ga kowa ba sai dai mutum ya kai kuɗinsa da kansa kamar yadda aka tsara da farko.

Buhari Ya Amince A Kashe Tsohuwar Naira 200

A wani jawabi da ya yi a yau Alhamis, shugaba ƙasa Muhammadu Buhari ya ba Babban Bankin Najeriya CBN umurnin sake fito da tsohuwar naira 200 a hannun al'umma domin ci gaba da amfani da ita har zuwa ranar 10 ga watan Afrilun wannan shekara. Buhari ya bayyana cewa an samu muhimman nasarori ta dalilin canjin fasalin kuɗi da aka yi. Ya nunar da cewa yana sane da irin halin matsin da 'yan Najeriya suka shiga, akan haka suna iya amfani da tsohuwar naira 200 sai dai su kai tsofaffin kuɗaɗe da suka haɗa da naira 500 da kuma naira 1000 a bankin CBN. Menene ra'ayinku kan wannan batu?

CBN Insists On Deadline Despite Court Order

The Central Bank of Nigeria CBN has insisted that its February 10th deadline for the validity of old naira notes still stands. The CBN governor, Godwin Emefiele, made the disclosure while briefing the diplomatic community at the ministry of foreign affairs in Abuja. The development comes despite the ex-parte order of the Supreme Court which restrained the federal government from implementing the February 10th deadline, pending the hearing of the matter on February 15th. Emefiele said the situation is substantially calming down since the commencement of over-the-counter payments to complement ATM disbursements and the use of super-agents. He added that there is no need to consider any shift from the deadline of February 10th.

Filin Jiragen Sama Na Malam Aminu Kano Zai Ci Naira Biliyan 700

Ministan suhurin jiragen sama Alhaji Hadi Sirika, ya bayyana cewa majalisar zartaswata ƙasa ta amince da ware fiye da naira biliyan ɗari bakwai domin aikin kwangilar gyaran filin sauka da tashin jiragen na sama na duniya na Malam Aminu Kano, wanda ya ce za kammala a cikin shekara ɗaya rak. Majalisar zartaswa ta ƙasa ta kuma amince da ware naira biliyan ɗari da goma sha bakwai domin gudanar da kwangilar gina cibiyar bincike akan man fetur ta Oloibir a yankin Naija Delta. Ministan ƙasa a ma’aikatar albarkatun man fetur, Timipre Sylva ne ya shaidawa ‘yan jaridar fadar shugaban ƙasa hakan, inda ya ce za a kammala aikin kwangilar a cikin shekaru biyu da rabi. Ya ce tun a 1980 gwamnatin Alhaji Shehu Aliyu Shagari ta soma aikin, amma daga bisani aka yi watsi da shi wanda a yanzu zai zama ɗaya daga cikin manyan ayyukan da za a ci ga da tunawa da shugaba Muhammadu Buhari a yankin Naija Delta mai arzikin man fetur.

Kotu Ta Tabbatar Da Peter Obi Matsayin Ɗan Takarar Jam'iyyar LP

Kotun ɗaukaka ƙara mai mazuninta a Abuja ta yi watsi da ƙarar da jam’iyyar APM ta shigar inda take neman a hanawa Peter Obi na jam’iyyar Labour damar tsayawa takara a zaɓe mai zuwa. Waɗanda ake ƙarar su ne Hukumar Zaɓe mai zaman kanta, INEC da jam’iyyar Labour da kuma ɗan takararta Mista Peter Obi. Da ta ke yanke hukuncin tare da taimakon alƙalai uku, mai shari’a Monica Dongban-Mensem, ta amince da yin watsi da shari’ar a dalilin rashin cikakkun hujjoji. Alaƙalan kotun sun nemi masu saka ƙarar da su biya waɗanda ake ƙara tarar naira dubu ɗari biyu a dalilin ɓata mu su lokaci.

Tinubu Zai Dawo Da Tsoffin Kuɗi - El-Rufai

Gwamnan jahar Kaduna Malam Nasiru Ahmed El-Rufai ya roƙi jama'a cewa kowa ya yi amfani da tsoffin kuɗi daga nan har shekara huɗu. A cikin wani gajeren bidiyo mai tsawon minti huɗu da daƙiƙa talatin da bakwai, an ga gwamnan na bayyana cewa ya bayar da umurnin duk wani ɗan jahar da ke kasuwanci kada ya fasa amfani da tsoffin kuɗaɗe. "Duk wani ɗan jahar Kaduna daga nan har shekara huɗu in dai an zaɓi APC, Uba zai mayar masa da kuɗinsa". In ji gwamna El-Rufai. A cewarsa wannan saƙo ne daga ɗan takarar jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, wanda kuma in ji gwamnan da an zaɓi Tinubu zai sauya wannan tsarin canjin fasalin kuɗi nan take in da zai dawo da tsoffin da mutane ba su kai banki ba. Saboda haka ya umurci jama'a da kada kowa ya kai kuɗinsa banki. Ya ƙara da cewa da zarar an zaɓe su, ya ɗauki alkawarin amsar kuɗin mutane ya tilasta Babban Bankin Najeriya CBN ya canza su musu da sababbi. Ya ci gaba da cewa, "Ku gaya ma kowane ɗan kasuwa, ya karɓi tsohon

PDP Na Shirin Korar Wike

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya shigar da ƙara domin hana wani sabon yunƙurin jam’iyyar PDP dakatar da shi daga cikinta, kuma ya buƙaci kotun da ta ɗauki mataki ga duk masu wannan aniya.  Ɗaya daga cikin jigajigan jam'iyyar PDP da suka mayar da martani kan ƙarar da gwamna Wike ya shigar, Mahdi Shehu, ya mayar da martani a ranar Litinin da ta gabata inda ya wallafa a shafinsa na twitter wata sanarwa cewa, “Wike ya shigar da ƙara kan jam’iyyar PDP mai lamba FHC/ABJ/CS/139/2023 ta hannun lauyoyinsa, DY Musa (SAN);  Douglas Moru, da C. C. Chibuike, yana neman a ba shi umarnin hana a kore shi daga PDP.”   Wike dai ya yi ta famar ruguza jam’iyyar har ma ya rasa inda za shi. Gwamnan na Ribas ya zamewa jam'iyyar PDP ƙadangaren bakin tulu, irin yadda ya ke uwa da makarbiya tun bayan da dangantaka ta soma tsami tsakaninsa da wasu jigajigan jam'iyyar ciki kuwa har da gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.  

Japan Ƙasar Da Kowa Tsoho

A ƙasar Japan da ke gabashin Asiya, adadin haihuwa a shekara ya ragu zuwa kasa da dubu 800 a karon farko a shekarar 2022. Ya zuwa farkon shekarar 2023, kashi 29 na al'ummar Japan mai mutane miliyan 124.77 na da shekaru 65 ne ko sama da haka, kuma kashi 11.6 na tsakanin shekarun 0 da 14. Japan ita ce ƙasa ta farko a duniya bisa ga jimillar yawan jama'a masu shekaru 65 zuwa sama. Firaministan ƙasar, Kishida Fumio ya sanar da cewa Japan na gab da rasa ayyukanta na zamantakewar al’umma sakamakon raguwar yawan haihuwa kuma a bana za su mai da hankali kan manufofin renon yara. Hukumar Kula da Yara da Iyali, mai alaƙa da gwamnatin ƙasar za ta fara aiki a watan Afrilu. Kisida ya bayyana cewa suna shirin ruɓanya kasafin kuɗin manufofin da suka wajaba daga yanzu zuwa watan Yuni. Duk da ci gaban da ƙasar Japan ke da shi a fannonin ƙere-ƙere da fasaha, rashin wadattatun matasa ya sa tana fuskantar matuƙar barazana ga ƙarewar jama'a.

Jam'iyyu 13 Sun Yi Barazanar Ƙauracewa Zaɓe A Najeriya

Gamayyar jam'iyyun adawa 13 sun bayyana cewa za su ƙauracewa shiga zaɓe muddin Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ƙara wa'adin amfani da tsofaffin kuɗaɗe daga lokacin da aka ɗiba tun da farko. Shugaban jam'iyyar AA Kennetth Udeze ne ya fitar da wannan sanarwa, in da ya ce canjin fasalin kuɗi da CBN ya fito da shi zai haifar da babban tasiri a tattalin arziki da fannin tsaro kana sun kai matsayar watsi da sabon matakin da gwamnonin APC suka ɗauka da suka haɗa da na Kaduna, Malam Nasiru El-rufai da na Zamfara Bello Mutawalle da na Kogi Yahaya Bello, na maka shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a gaban kotu kan sauya takardun kuɗi da ya yi. A Najeriya akwai jerin jam'iyyu 18 da za su fafata a babban zaɓe mai zuwa sai dai 13 daga ciki sun yi barazanar janye jikinsu daga shiga zaɓen muddin aka ƙara lokacin amfani da tsofaffin kuɗaɗe. Menene ra'ayinka kan wannan batu?

Yadda Masu Kuɗi Da Ruwa Suka Cika Harabar ATM

Rahotonni da ke ci gaba da shigo muna yanzu haka, na nuni da cewa ɗaruruwan mutane na ta yi dogayen  layuka a gaban na'urar cirar kuɗi ta ATM da ke bankuna, inda suke amfani da wani salo na biyan mutane domin su ciro mu su kuɗi. Wani da muka zanta da shi mai suna Lawal Mai Masara, ya shaida muna cewa, tun jiya ya ke kan layi, kuma har yanzu bai kai ga samun kuɗin ba saboda masu sana'ar POS da masu kwashe kuɗi su sake adanawa sun cika ko'ina. "Za ka ga mutane riƙe da katunan cirar kuɗi fiye da 10 inda suke tura ma wasu kuɗi su rarraba musu katunan domin a cire mu su kuɗin a ATM daga baya su bayar da naira dubu akan duk dubu goma da aka cire mu su". In ji shi. Mutumin ya ƙara da cewa wannan na daga cikin manyan dalilan da suka haddasa ƙarancin kuɗi tsakanin mutane a Najeriya.musamman arewa. Wannan sabon matakin ya nuna irin yadda mutane ke jefa kansu a halin tasku ta hanyar ci gaba da kwashe kuɗaɗen da jama'a ya kamata su samu. Wani ganau

Wike Ya Tona Magoya Bayan Atiku A Fadar Shugaban Ƙasa

Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, ya ce abubuwan da suka faru a baya-bayan nan sun tabbatar masa da cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar da magoya bayansa, na taƙama da cewa ba sa buƙatar goyon bayan gwamnonin G5 kafin su ci nasara zaɓe, saboda wasu tsiraru a fadar shugaban ƙasa sun ba su tabbacin samun nasara a zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa. Jaridar POLITICS NIGERIA  ta ruwaito cewa gwamnan yayi magana ne a garin Ibaka a yayin gangamin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar PDP reshen jihar Ribas na ƙaramar hukumar Okrika a ranar Juma’a. "Na ce an ba su tabbaci, amma wannan zaɓen ba zai dogara ne akan wannan tabbacin ba, yana kan tabbacin mutane ne,” in ji Wike. Gwamna Wike dai ya dage cewa har yanzu Atiku na buƙatar jihar Ribas don samun nasara ko kuma ya faɗi zaɓe a 2023. A cewarsa, “ko kuna so ko ba ku so, dole ne ku buƙaci jihar Ribas. Idan ba ku buƙatar Jihar Ribas to dole ne ku sha ƙasa. Idan kun ce ba ku son mu, lallai kuwa za ku gaz

Canjin Kuɗi Alfanu Ne - Peter Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar Labour Party Mista Peter Obi, ya shawarcin 'yan Najeriya da su rungumi sabon tsarin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya fito da shi na canjin fasalin kuɗi, in da ya ce yana da muhimmanci. Ya roƙi 'yan Najeriya da su marawa tsarin baya, wanda a cewar sa  ba Najeriya ce ta farko a canza fasalin kuɗi ba a duniya, sai dai wannan ya zo da wahala ga jama'a amma kuma yana da matuƙar amfani ga tattalin arzikin ƙasa  da walwalar jama'a duk da akwai buƙatar a inganta shi. Mista Obi ya bayyana hakan a shafinsa na twitter a ƙarshen makon nan. Peter Obi dai ya taɓa zama mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar a 2019 kafin yanzu shi ma ya fito neman wannan kujera a babban zaɓe mai zuwa.

INEC Ta Yaba Yadda Na'urar BVAS Ke Aiki

Shugaban Hukumar Zaɓe INEC Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa gwajin da aka yi na tantance masu jefa kuri'a ya nuna na'urar BVAS da aka fito da ita na yin aiki yadda ya dace. Shugaban hukumar ya bayyana hakan yayin da ya ke ganawa da manema labarai a birnin Tarayya Abuja. Ya ce "naurar na iya tantance masu zaɓe cikin dakika 30 kuma babu wata alamar tasgaro a tattare da ita". Farfesa Yakubu ya ce sun tanadi na'urorin wucin gadi ko da aka yi wasu daga cikin na'urorin su kasa lokacin da ake tantance mazu jefa kuri'a da su.