Skip to main content

Tinubu Zai Dawo Da Tsoffin Kuɗi - El-Rufai

Gwamnan jahar Kaduna Malam Nasiru Ahmed El-Rufai ya roƙi jama'a cewa kowa ya yi amfani da tsoffin kuɗi daga nan har shekara huɗu.
A cikin wani gajeren bidiyo mai tsawon minti huɗu da daƙiƙa talatin da bakwai, an ga gwamnan na bayyana cewa ya bayar da umurnin duk wani ɗan jahar da ke kasuwanci kada ya fasa amfani da tsoffin kuɗaɗe.
"Duk wani ɗan jahar Kaduna daga nan har shekara huɗu in dai an zaɓi APC, Uba zai mayar masa da kuɗinsa". In ji gwamna El-Rufai.
A cewarsa wannan saƙo ne daga ɗan takarar jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, wanda kuma in ji gwamnan da an zaɓi Tinubu zai sauya wannan tsarin canjin fasalin kuɗi nan take in da zai dawo da tsoffin da mutane ba su kai banki ba. Saboda haka ya umurci jama'a da kada kowa ya kai kuɗinsa banki.
Ya ƙara da cewa da zarar an zaɓe su, ya ɗauki alkawarin amsar kuɗin mutane ya tilasta Babban Bankin Najeriya CBN ya canza su musu da sababbi.
Ya ci gaba da cewa, "Ku gaya ma kowane ɗan kasuwa, ya karɓi tsohon kuɗi, Nasiru El-Rufai da Uba Sani da Bola Ahmed Tinubu, sun yi muku alkawari, in dai an zaɓe mu, wannan tsari za a canza shi a ba kowa iya lokacin da ya kamata ya canza kuɗinsa".
Wannan na zuwa kwana ɗaya da babbar kotun tarayya ta ba shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da Babban Bankin CBN umurnin kada su ƙara wa'adin amfani da tsoffin kuɗaɗe.
Sai dai kafin nan gwamna El-Rufai na cikin na gaba wajen ƙalubalanatar shugaban ƙasa da Babban Bankin CBN akan sauyin fasalin kuɗi da har ya jagoranci wata tawaga da ta haɗa gwamnonin jahohin Kogi da Zamfara in da suka gana da shugaban ƙasa kan wannan batu, kafin daga bisani su maka Bankin CBN da shugaban ƙasa kotu.
A na haka wasu gamayyar jam'iyyu 13 sun fito sun bayyana cewa za su janye daga shiga zaɓe mai zuwa muddin aka ɗaga wa'adin da Bankin CBN ya ƙayyade na amfani da tsoffin kuɗaɗe daga ranar 10 ga wannan wata na Fabrairu.
Ko a ranar jiya Talata ƙungiyar gwamnoni sun gana da shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emefiele da kuma shugaban Hukumar EFCC a fadar Villa akan batun da ya shafi ƙarancin kuɗi a hannun jama'a da kuma buƙatar a ƙara wa'adin amfani da tsoffin kuɗi, zaman da aka tashi baram-baram.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

An Sako Ƙarin Fasinjojin Jirgin Ƙasa Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Wasu fasinjoji bakwai da aka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na ranar 28 ga Maris a jihar Kaduna sun samu 'yanci. An sako mutanen ne a safiyar Laraba bayan sun shafe kwanaki 135 a hannun ‘yan ta’addan. Sai dai ba a bayyana ko an biya kudin fansa ga 'yan ta'addar domin a sako su ba. Ɗaya daga waɗanda suka shiga sasantawar mai suna Tukur Mamu, ya fada  a wata sanarwa a ranar Laraba cewa shida daga cikin wadanda aka sako ‘yan gida daya ne, wadanda suka hada da ma’aurata da ‘ya’yansu hudu.  Sanarwar ta ce an sako yaran da iyayensu ne bayan da Sheik Ahmad Gumi ya shiga tsakani

Wanene Ɗan Jarida?

Ɗan jarida mutum ne kamar kowa, sai dai tunaninsa da manufofinsa kan tafi daidai ne kawai da ra'ayin MASU SAURARO ta fuskokin da suka shafi aikinsa. Ya zama mai wakiltar waɗanda ba su da baki ne ko kafafuwan zuwa, kuma idanuwan talakawa a kowane lokaci. Idan ka nuna ma sa launi shuɗi, ƙoƙarin ya ke ya tabbatar da launin nan shuɗi ne ziryan ko yana da garwaye? Idan ka ce ma sa labarin abu kaza ya faru, ba zai ce a'a ba kuma ba zai ce eh ba, aikinsa shi ne TABBATARWA . Idan mai sauraro namiji ne ko mace ko mai ra'ayin wani addini ko akida ko mai kuɗi ko talaka, ɗan jarida kan GIRMAMA kowa, kuma zai ɗauki kowa a matsayin DAIDAI ta fuskar ba su damar bayyana ra'ayoyinsu. Ɗan jarida kan tafi da zamani, ya kuma rungumi fasahar da ƘIRƘIRA ta kawo domin tafiya daidai lokaci. A kowace marra GASKIYA ita ce madogarar ɗan jarida, kuma wannan kan ƙara sa masu sauraro su amince da shi. Amma kuma, dole ne ɗan jarida ya zama MAI IKON KANSA , ba zai yi ma kowa alfarma b...