Skip to main content

'Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidajen Ma'aikatan Filayen Jiragen Saman Najeria Tare Da Sace Mutum 11


Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari a gidajen ma'aikatan Hukumar Filin Jirgin Saman Tarayyar Najeriya da ke Kaduna, inda suka yi awon gaba da akalla mutane 11.
Rahotannin baya-bayan nan sun kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi nasarar sace ma’aikacin Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NAMA)A, da matarsa, da jami’in Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NIMET) da ya’yansa, kuma har yanzu ba a san inda suke ba.
Satar mutane ya zama ruwan dare a Najeriya a yau, kuma kusan kowace safiya ana samun rahotannin kashe-kashe ko satar mutane don neman kudin fansa. 
A makon da ya gabata ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin kawo karshen satar mutane a Najeriya amma ga dukkan alamu kalaman nasa ba su yi tasiri ba.





Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey