Skip to main content

Posts

Showing posts from December 22, 2020

An Rufe Makarantu Da Wuraren Holewa A Najeriya

Sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya Boss Mustapha ne ya bayar da umurnin a jiya, cewa dukan makarantu da wuraren shakatawa za su kasance a rufe har tsawon makonni biyar. Gwamnatin ta kuma bayar da umurnin ma'aikata daga mataki na 12 zuwa kasa su yi zaman su a gida, in ban da ma su aikin gaggawa, kamar jami'an kiyon lafiya da sauran su. Wannan matakin ya biyo bayan yadda annobar korona ke ci gaba da hayyaka a Najeriya. Haka ma an jiyo ministan lafiyar kasar Osagie Ehanire na bayar da umurnin sake bude cibiyoyin killace wadanda suka kamu da cutar. Tuni dai wasu jahohin kasar da suka hada da Legas, Kaduna da Imo suka bayar da damar rufe makarantu tare da gindaya dokoki da ka'idojin yaki da cutar, ta hanyar rufe wuraren rawa da takaita zirga-zirga da kayyade lokacin halartar wuraren ibada da ma saka takunkumi.

Sabuwar Kwayar Cutar Korona Ta Soma Yaduwa

A farkon makon nan a ka gano wata nau'in kwayar cutar korona da ta sha bamban da wacce aka sani. Ita dai wannan sabuwar kwayar cuta ta bulla ne a kasar Burtaniya, in da ta yi nasarar mamaye birnin Landan da gasbascin kasar a yankunan Surrey, Essex, Backshire, Backinghamshire Kent da sauran su. Firaminstan kasar Boris Johnson ya ce a halin da ake ciki yanzu, kwayar cutar na bazuwa ne cikin sauri fiye da ta farko; wanda yanzu haka ta ke kashi 70 cikin dari a mizanin yaduwa. Masana kiyon lafiya a duniya sun bayyana cewa, ba Burtaniya kadai wannan sabuwar korona ta bulla ba, har da da Afirka ta kudu da ma sauran sassan duniya kawai dai ba a kai ga farga da hakan ba ne. A cewar su, Burtaniya dai ce ta yi kwakkafin gano ta saboda tsananin bincike da gwajin da ta fi kowace kasa yi kan wannan cuta. Tuni dai kasashen duniya da suka hada da Jamus, Faransa, Italiya, Austireliya, Iceland, Spaniya, Saudiyya da sauran su, suka dakatar da zirga zirgar jiragen sama tsakaninsu da kasar