Skip to main content

Posts

Showing posts from May 12, 2022

An Kashe Wata Daliba Da Aka Zarga Da Batanci Ga Manzon Allah A Jahar Sokoto

Wata dalibar Kwalejin Ilmi ta Shehu Shagari da ke Sokoto, mai suna Debora Samuel, ta gamu da ajalinta lokacin da wasu matasa da ba a kai ga sanin ko su wanene ba suka kashe ta hanyar kona ta, bayan da aka zarge ta da yin batanci ga Annabi mai tsira da amincin Allah. Lamarin ya kazance ne bayan da wasu daga daliban kwalejin suka yi zargin cewa ta dade ta na wannan batancin abinda ya kai ga barkewar rikicin da ya kai ga salwantar ranta. Tuni dai mahukuntan jahar Sokoto suka bayar da sanarwar rufe kwalejin har a kammala bincike. Babban sakatare a ma'aikatar ilmi mai zurfi ta jahar Sokoto Alhaji Almustapha Usman Ali, ya shaidawa manema labarai cewa, an bayar da umurnin rufe kwalejin kazalika za su sanar da jama'a mataki na gaba idan har an kammala bincike. An dai girke jami'an tsaro a harabar makarantar domin dakile rikicin da ka iya tasowa. Tuni dai da hotunan bidiyo da Tantabara ba ta kai ga tantantace sahihancinsu ba, suka karade shafukan sada zumunta, wadanda k