Skip to main content

Posts

Showing posts from February 7, 2023

PDP Na Shirin Korar Wike

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya shigar da Æ™ara domin hana wani sabon yunÆ™urin jam’iyyar PDP dakatar da shi daga cikinta, kuma ya buÆ™aci kotun da ta É—auki mataki ga duk masu wannan aniya.  ÆŠaya daga cikin jigajigan jam'iyyar PDP da suka mayar da martani kan Æ™arar da gwamna Wike ya shigar, Mahdi Shehu, ya mayar da martani a ranar Litinin da ta gabata inda ya wallafa a shafinsa na twitter wata sanarwa cewa, “Wike ya shigar da Æ™ara kan jam’iyyar PDP mai lamba FHC/ABJ/CS/139/2023 ta hannun lauyoyinsa, DY Musa (SAN);  Douglas Moru, da C. C. Chibuike, yana neman a ba shi umarnin hana a kore shi daga PDP.”   Wike dai ya yi ta famar ruguza jam’iyyar har ma ya rasa inda za shi. Gwamnan na Ribas ya zamewa jam'iyyar PDP Æ™adangaren bakin tulu, irin yadda ya ke uwa da makarbiya tun bayan da dangantaka ta soma tsami tsakaninsa da wasu jigajigan jam'iyyar ciki kuwa har da gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal.  

Japan Ƙasar Da Kowa Tsoho

A Æ™asar Japan da ke gabashin Asiya, adadin haihuwa a shekara ya ragu zuwa kasa da dubu 800 a karon farko a shekarar 2022. Ya zuwa farkon shekarar 2023, kashi 29 na al'ummar Japan mai mutane miliyan 124.77 na da shekaru 65 ne ko sama da haka, kuma kashi 11.6 na tsakanin shekarun 0 da 14. Japan ita ce Æ™asa ta farko a duniya bisa ga jimillar yawan jama'a masu shekaru 65 zuwa sama. Firaministan Æ™asar, Kishida Fumio ya sanar da cewa Japan na gab da rasa ayyukanta na zamantakewar al’umma sakamakon raguwar yawan haihuwa kuma a bana za su mai da hankali kan manufofin renon yara. Hukumar Kula da Yara da Iyali, mai alaÆ™a da gwamnatin Æ™asar za ta fara aiki a watan Afrilu. Kisida ya bayyana cewa suna shirin ruÉ“anya kasafin kuÉ—in manufofin da suka wajaba daga yanzu zuwa watan Yuni. Duk da ci gaban da Æ™asar Japan ke da shi a fannonin Æ™ere-Æ™ere da fasaha, rashin wadattatun matasa ya sa tana fuskantar matuÆ™ar barazana ga Æ™arewar jama'a.