Skip to main content

Posts

Showing posts from February, 2021

Da Dumi Dumi An Saka Ranar Mukabila Da Malam Abduljabbari Kano

Gwamnatin jahar Kano ta bakin kwamishinan watsa labaran jahar,  Muhammad Garba  da na ma'ikatar addin musulunci Muhammad Tahar ne suka sanar da kafar BBC Hausa lokacin da za a gudanar da mukabila da Malam Abduljabbar Nasiru Kabara. Bangaren gwamnatin ya fitar da ranar lahadi 7 ga watan gobe na Maris a matsayin ranar da malaman jahar Kanon za su gwabza da Malamin. Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kuma yi alkawarin samar da cikakken tsaro a lokacin gudanar da muhawarar ta ilmi. Wannan bukatar da malamin ya dade yana nema sai a wannan karo ya samu amincewar gwamnati a hukumance. TANTABARA za ta kawo muku yadda muhawarar za ta kasance.

Da Dumi Dumi Manyan Sojoji Sun Mutu A Wani Hadarin Jirgin Saman Sojan Najeriya

Rahotannin da ke shigowa yanzu haka sun tabbatar da faduwar wani jirgin saman soji kirar Boeng 350, daf da filin jiragen sama na Abuja, wanda wata majiya ke cewa na kan hanyarsa ne ta zuwa Mina ta jahar Naija. Ministan suhurin jiragen sama Hadi Sirika ya tabbatar da aukuwar lamarin, ta shafinsa na tweeter, in da ya ce an samu bayanin lalacewar dayan injimini jirgin tun farkon tashinsa. Wasu bayanan na daban sun ce ana fargabar akalla mutum 14 sun hallaka da suka hada masu mukamin janar biyu, da kaftin hudu, kofura biyu hadi da ma'aikatan jirgin hudu. An dai ga wuta na ci tare da tashin hayaki da ya game wurin, a daidai lokacin da jami'an kwana-kwana ke kokarin kashe wutar.

Alamu Na Nuna Gwamna Wike Zai Shiga APC

Bayanai da ke fitowa yanzu haka na bayyana alamun gwamnan jahar Rivers Nyesom Wike na daf da tsunduma jam'iyar APC mai mulki. An jiyo babban mai tsawatawa na majalisar wakilai ta tarayya Orji Uzo Kalu na bayar da tabbacin cewa tattaunawa ta yi nisa tsakaninsa da gwamna Wike. Kalu ya sanar da manema labaru a ranar alhamis cewa, bayan da gwamnan ya gayyace shi rangadin wasu ayukka da ke gudana a babban birnin jahar Fatakwal, ne suka tattauna kan wannan batun. Orji Kalu ya kuma ce sun shafe daren ranar suna shawarwari da gwamnan akan yadda zai shigo kana ya karfafa masa guiwa kan shiga jam'iyar APC, domin jawowa jahar ta Rivers alhairai masu yawa daga gwamnatin tarayya, in da kuma ya nuna yayi na'am da wannan shawara.

Shak Ahmad Gumi Ya Fara Tattaunawa Da wadanda Suka Sace Yaran Makarantar Kagara

Malamin ya sanar da cewa maharan da suka sace daliban wata Makaranta da ke Kagaran jahar Naija, sun kira shi domin ya nemo gwamnati a tattauna yadda za a saki yaran. Shak Ahamd Gumi ya ce, shi kan sa bai san in da maharan ke fakewa ba, amma dai ya samu tattaunawa ta waya da shugaban 'yan fashin da suka addabi yankunan arewacin Najeriya, mai suna Dogo Gide, in da ya sanar da malamin alkawarin da suka dauka na tattaunawa da gwamnati. To amma kuma har yanzu bangaren gwanatin tarayya da ma jahohi ba su ce uffan ba kan wannan batu. Duk dai kokarin da jami'an tsaro na gano in da wadannan mahara ke fakewa a dazuka ya ci tura, amma a galibin lokuta Shak Ahmad Gumi ya sha kutsa kai a dazuka da zimmar ilmantar da su da kuma nan shiga tsakani don neman sulhu.  Sai dai a duk wannan kokari da Ahmad Gumi ya nuna yana yi hare-haren 'yan bindiga sai karuwa suke, inda wannan kwashe dalibai a makarantun kwana shi ne na hudu baya ga makarantar Kankarar jahar Katsina kimanin watann

An Ruguza Makarantar Malam Abduljabbar Kano

Dazu dazun nan gwamnatin jahar Kanon ta tura jami'an ma'aikatar lura da tsarin filaye in da ta ruguza makarantar Malam Abduljabbar. Gwamnatin dai ta taba bayyana cewa filin da ya ke amfani da shi haramtacce ne, in da ta kai ga kwace shi tare da bada umurnin gudanar da wasu muhimman ayukka a wurin. Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin gwamnatin jahar Kano da Abduljabbar in da a ranar laraba sakataren watsa labaran gwamnatin jahar, Muhammad Garba ya bayar da sanarwar rufe masallacin Malam Abduljabbar tare da hana masa gudanar da wa'azi baki daya. In da ta ce hakan na da alaka da irin yadda ya ke tunzura jama'a a kalaman da ya ke amfani da su a lokacin da ya ke da'awa.

TAURARUWA MAI WUTSIYA... GANDUJE KO ABDULJABBARI?

RA'AYI: Dambarwar da ta dabaibaye batun nan na dakatar da Abduljabbar Nasiru Kabara a jahar Kano na ta jan hankalin al'umma a kwanan nan. Lamarin ya ja ra'ayin masana da masu sharhi na ta tofa albarkacin bakinsu kan batun. Wannan ya sa jaridar Tantabara News ta yi tsokaci akan yadda masana da tarihi ya hango makomar irin wadannan mutane. A ranar larabar makon jiya ne gwamnatin jahar Kano ta dauki matakin rufe masallacin da malamin ke da'awa da aka fi sani da suna As-habul Kahf da ke takiyar birnin Kano. Haka ma gwamnatin ta hana ma sa yin da'awar tare da yi ma sa wani abu mai kama da daurin talala; da ta bayyana da cewa kandagarki ne ga irin matakan da aka lura ya na dauka na hargitsa jama'a tare da boyayyar manufa mai jirwaye kama da wanka.   Wanene Abduljabbar Nasir Kabara?  Abduljabbari dai matashin malami ne mai dimbin magoya baya, mai son daukaka da suna a kafofin sada zumunta na zamani da kafar sadarwa ta YouTube mai kare mashabar Shi'a aka

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Abduljabbar Nasir Kabara Daga Yin Wa'azi, Ta Rufe Masallacinsa

Malamin nan da aka fi sani da ra'ayi na daban da ke tsaka-tsakin mashabar Shi'a da Darika da ya ke da'awar cewa yake bi. Ya dai hadu da hushin gwamnatin jahar Kano sakamakon kalamansa da gwamnatin ta bayyana da cewa za su iya haddasa fitina a jahar. Abduljabbar Kabara dai sananne ne a kafofin sada zumunta da kuma shafukan YouTube in da ya ke watsa kalamansa da bincike ya tabbatar da sun fi karkata wajen zagin sahabbai, abinda kuma galibin jama'a da malamai suka ce ra'ayi ne irin na Shi'a. Gwamnatin dai ta bakin kwamishinan watsa labaran jahar Muhammad Garba, ta tabbatar da wannan umurnin. Ya kuma kara da cewa an ba kwamishin 'yan sandan jahar umurni da nan take ya tabbatar da an rufe masallacinsa mai suna As-habul Kaf da ke unguwar Gwale, a tsakiyar birnin Kano, tare da bayar da umurnin hana masa duk wani abu da ya kira wa'azi. Sai dai yayin da wannan umurnin ya zo a daren laraba, wasu na ganin batun bai rasa alaka da siyasa, to