Skip to main content

Shak Ahmad Gumi Ya Fara Tattaunawa Da wadanda Suka Sace Yaran Makarantar Kagara

Malamin ya sanar da cewa maharan da suka sace daliban wata Makaranta da ke Kagaran jahar Naija, sun kira shi domin ya nemo gwamnati a tattauna yadda za a saki yaran.
Shak Ahamd Gumi ya ce, shi kan sa bai san in da maharan ke fakewa ba, amma dai ya samu tattaunawa ta waya da shugaban 'yan fashin da suka addabi yankunan arewacin Najeriya, mai suna Dogo Gide, in da ya sanar da malamin alkawarin da suka dauka na tattaunawa da gwamnati.
To amma kuma har yanzu bangaren gwanatin tarayya da ma jahohi ba su ce uffan ba kan wannan batu. Duk dai kokarin da jami'an tsaro na gano in da wadannan mahara ke fakewa a dazuka ya ci tura, amma a galibin lokuta Shak Ahmad Gumi ya sha kutsa kai a dazuka da zimmar ilmantar da su da kuma nan shiga tsakani don neman sulhu. 
Sai dai a duk wannan kokari da Ahmad Gumi ya nuna yana yi hare-haren 'yan bindiga sai karuwa suke, inda wannan kwashe dalibai a makarantun kwana shi ne na hudu baya ga makarantar Kankarar jahar Katsina kimanin watanni biyu da suka gabata, in da wasu mahara suka yi garjuwa da dalibai 344 a dajin Tsafe ta jahar Zamfara.
Masana na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan wannan lamari mai daure kai, in da ko jiya an jiyo fitaccen lauyan nan Barista Bulama Bukarti na shedawa BBC Hausa cewa, akwai lauje cikin nadi a yadda wadannan mahara suka mayar da wannan garkuwa da jama'a a matsayin sana'a.
Kawo yanzu dai ba a san wane irin sulhu maharan ke nema a yi ba alhali suna rike da yaran.
Amma dai malamin ya ce maharan sun koka a kan yadda jami'an tsaro ke addabar su idan sun shigo gari. Kazalika, ana yawan kai mu su hari abinda a cewarsu muddin ba daina ba to ba za a zauna lafiya ba; sai dai bangaren jami'an tsaron Najeriya ba su bayyana ko za su daina kaiwa mayakan hari ba.
A jiya dai ne ministan tsaron Najeriya Bashir Magashi ya fito fili ya bayyana cewa bai dace jama'a su dinga gudun maharan ba, a maimakon haka ya kamata su yaki 'yan bindigar, kalaman da suka jawo cece-kuce tsakanin 'yan Najeriya da ke cewa akwai alamun gwamnatin Najeriya ta kasa a bangaren tsaro. 

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...