Skip to main content

Posts

Showing posts from March 23, 2022

An Tilas Ni Tsayawa Takara - In Ji Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana bukatar tsayawa takarar shugaban kasa a 2023 karkashin babbar jam'iyyar adawa ta PDP a karo na biyar, in da ya ce ya wajaba ne ya karba kiran jama'a. Atiku ya yi wannan magana ne a birnin tarayya Abuja lokacin da ya ke sanar da muradin nasa, "Abubuwan da suka ja hankalina na da yawa, muhimmai daga cikin su akwai bukatar samar da hadin kai, tsaro da tattalin arziki, ciyar da bangarorin gwamnatin tarayya gaba da sauran su". Atiku Abubakar na bayyana wannan ne daidai lokacin da gwamnan jahar Sokoto kuma tsohon kakakin majalisar wakilai ta kasa Aminu Waziri Tambuwal shi ma ya bayyana anniyarsa ta tsayawa neman shugabancin Najeriya a karkashin jam'iyyar ta PDP. Tambuwal ya ce babu wani da ya fi dacewa ya mulki kasar nan a wannan lokaci da ake ciki idan ba shi ba. Ya bayyana kan sa a matsayin matashi kuma wanda ya goge a harkar siyasa masanin dubarun mulki da ya san makomar Najeriya

Dole Mai Son Tsayawa Takara Ya Sauka - 'Yan Majalisar Najeriya

'Yan majalisar dattawa da na wakilan Najeriya sun hada guiwa in da suka gudanar da zaman majalisar ranar laraba 22.03.2022 a zaure guda, domin kalubalantar wani hukucin da ke barazana ga dokar da suka kaddamar. Mahukuntan sun yi watsi da hukuncin babbar kotun tarayya reshen jahar Abiya, da ta umurci ministan shari'a Abubakar Malami ya goge sashe na 84 (12) na kundin tsarin mulkin 1999, wanda ya haramta ma masu rike da mukamin siyasa tsayawa takara ko jefa kuri'a, kuma ya wajabta ma duk wanda ke neman a zabe shi a 2023 da ya sauka wata shida kafin zabe. Wannan ya jawo cece-ku-ce har ta kai shugaban kasa neman su yi ma dokar kwaskwarima, abinda kuma su ka ki amincewa da shi. A makon jiya dai babban mai sa kara na kasa, Abubakar Malami ya fito ya nuna amincewa da hukuncin babbar kotun, in da ya dauki alkawarin goge dokar. To amma kuma masana harkar shari'a sun yi ca kan wannan hukuncin tare da cewa ya sabawa doka. Fitaccen babban lauyan Najeriya Femi Falana, ya