Skip to main content

Dole Mai Son Tsayawa Takara Ya Sauka - 'Yan Majalisar Najeriya

'Yan majalisar dattawa da na wakilan Najeriya sun hada guiwa in da suka gudanar da zaman majalisar ranar laraba 22.03.2022 a zaure guda, domin kalubalantar wani hukucin da ke barazana ga dokar da suka kaddamar.
Mahukuntan sun yi watsi da hukuncin babbar kotun tarayya reshen jahar Abiya, da ta umurci ministan shari'a Abubakar Malami ya goge sashe na 84 (12) na kundin tsarin mulkin 1999, wanda ya haramta ma masu rike da mukamin siyasa tsayawa takara ko jefa kuri'a, kuma ya wajabta ma duk wanda ke neman a zabe shi a 2023 da ya sauka wata shida kafin zabe.

Wannan ya jawo cece-ku-ce har ta kai shugaban kasa neman su yi ma dokar kwaskwarima, abinda kuma su ka ki amincewa da shi.

A makon jiya dai babban mai sa kara na kasa, Abubakar Malami ya fito ya nuna amincewa da hukuncin babbar kotun, in da ya dauki alkawarin goge dokar. To amma kuma masana harkar shari'a sun yi ca kan wannan hukuncin tare da cewa ya sabawa doka. Fitaccen babban lauyan Najeriya Femi Falana, ya bayyana cewa, babban kiskure ne alkaliyar ta tafka.
Ya kara da cewa, "Idan a ka yi duba da waɗannan sassan na kundin tsarin mulkin Najeriya, lallai mai shari'a tayi babban kuskure wajen yanke hukuncin sassa na 66 (1) (f), 107(1) (f),137 (1) (f) da182 (1) (f) domin waɗannan sassan da mai shari'a ta yi amfani da su su na magana ne a kan ma'aikatan gwamnati ba masu riƙe da muƙamin siyasa ba".

Yanzu dai gamayyar 'yan majalisar dattawan da wakilai duk bakinsu ya zo daya in da suka kalubalanci hukuncin tare da shirin gatzayawa kotu.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey