Skip to main content

Posts

Showing posts from January 19, 2021

Biden Ya Nemi Magoya Bayansa Su Tsaya A Gida Lokacin Rantsar Da Shi

A daidai lokacin da ake daf da rantsar da sabon shugaban Amurka Joe Biden, an baza dubban jami'an tsaron soji domin murkushe duk wata zanga-zanga da ka iya barkewa. Tun a farkon makon da ya gabata ne dai Hukumar Leken Asiri ta Amurka ta FBI, ta yi gargadin cewa akwai yuwar samun tarzoma a ko'ina a kasar. Zababben shugaban dai ya shawarci jama'a da su yi zaman su a gida ba sai sun halarci bukin rantsarwar ba, ko baya ga matsalar annobar korona akwai yuwar dakarun sojin da aka baza na shirin maganin duk wanda ya nemi daukar dala ba gammo. Shugaba Donald Trump mai barin gado ya bayyana cewa zai bar babban birnin kasar Washington DC tun da sanyin safiyar gobe laraba, don kaucewa yin ido biyu da wanda zai gaje shi. A tarihin kasar dai wannan ne karon farko da za a yi bukin rantsarwa mafi tsaurin tsaro a Amurka, da kuma armashinsa ya ragu, muddin ta tabbata bai samu halarcin jama'a ba.

Akwai Yuwar Sake Rufe Makarantu A Nijeriya Saboda Korona

A irin yadda cutar korona ke ci gaba da kamari a duniya, mai yuwa kwamitin da shugaban kasa ya kafa don yaki da cutar na shirin bayar da shawara don sake kulle makarantu da zaran aka ga alkalumman masu kamuwa da ita na ci gaba da karuwa. An dai bude makarantun ne a ranar 18 ga wannan wata na Janairu, koda ya ke gwamnonin jahohin Kaduna da Edo ba su amince da bude makarantun ba. Ministan Ilmi Malam Adamu Adamu da sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha sun gana da shuwagabannin kwamitin yaki da annobar korona don daukar mataki na gaba, da ake jin bai rasa alaka da sake rufe makarantun. Bayan bude makarantu a jiya, galibin al'ummar kasar sun yi suka akan matakin, da suka ce mai hadarin gaske ne saboda abu ne mai wuya hukumomin makarantu a Najeriya su iya cika ka'idojin da aka gindaya, kasancewar ajujuwa a makarantun makare suke da dalibai da zai yi wahala a bada tazara tsakani.

Wasu Daga Hotunan Gobarar Kasuwar Sokoto

DA DUMI DUMI Gobara Ta Kama A Babbar Kasuwar Sokoto

Tun da sanyin safiyar yau gobarar ta tashi a bangaren masu kayan robobi da ke Babbar Kasuwar Jahar Sokoto, abinda ya haddasa hasarar dukiyar da ba a kai ga gano adadinta ba a halin yanzu. Babbar matsalar da ake fuskanta ita ce rashin hanyar da motocin kashe gobara za su bi, wanda wannan ya kara hayyaka matsalar gobarar da ke ci gaba da yaduwa zuwa wasu sassan kasuwar. Wannan ya sa masu dukiyar da ke ci gaba da konewa rashin sanin madogara, face diban kayansu da hannuwa ko don tsira da wani abu. Wasu da TANTABARA ta samu zantawa da su, sun bayyana cewa su kam sun tafka hasara, domin karfin wutar ba zai bar su fitar da wasu muhimamman abubuwa ba. To sai dai babu wani rahoton jikkata ko rasa rai kawo yanzu, wanda shi ne abinda ake fata.