Skip to main content

DA DUMI DUMI Gobara Ta Kama A Babbar Kasuwar Sokoto

Tun da sanyin safiyar yau gobarar ta tashi a bangaren masu kayan robobi da ke Babbar Kasuwar Jahar Sokoto, abinda ya haddasa hasarar dukiyar da ba a kai ga gano adadinta ba a halin yanzu.
Babbar matsalar da ake fuskanta ita ce rashin hanyar da motocin kashe gobara za su bi, wanda wannan ya kara hayyaka matsalar gobarar da ke ci gaba da yaduwa zuwa wasu sassan kasuwar.
Wannan ya sa masu dukiyar da ke ci gaba da konewa rashin sanin madogara, face diban kayansu da hannuwa ko don tsira da wani abu.
Wasu da TANTABARA ta samu zantawa da su, sun bayyana cewa su kam sun tafka hasara, domin karfin wutar ba zai bar su fitar da wasu muhimamman abubuwa ba.
To sai dai babu wani rahoton jikkata ko rasa rai kawo yanzu, wanda shi ne abinda ake fata.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey