Skip to main content

An Gano Wani Rini Na Zamanin Annabi Dawuda

Wata jaridar kasar Isra'ila mai suna Hamodia ta wallafa labarin mai ban mamaki da ya ja hankalin duniya a makon nan.
Masu hakar kayan tarihi da hadin guiwa da Jami'ar Barllan da kuma Jami'ar birnin Tel-Aviv ne suka samu nasarar gano wannan rinin mai lainin shudi, da shuni hade da saheti da aka ce ya kai shekaru dubu daya kafin bayyanar annabi Isa (a.s.) da kuma mazauna wani kwari da ake kira Slaves Hill da ke lardin Timna ke rinawa a lokacin.
Wani masani na Jami'ar Barllan Dakta Naama Sukenik da Dakta Erez Ben-Yosef, sun bayyana cewa rinin, mai matukar darajar gaske an samar da kayan hadinsa ne daga kwanson dodon kodi. Kuma an wallafa bayanin a mujallar PLOS ONE.

Comments

Unknown said…
Abin mamaki baya karewa a Duniya.
Unknown said…
Wow!Wonders never end.

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey