Skip to main content

TAURARUWA MAI WUTSIYA... GANDUJE KO ABDULJABBARI?

RA'AYI:
Dambarwar da ta dabaibaye batun nan na dakatar da Abduljabbar Nasiru Kabara a jahar Kano na ta jan hankalin al'umma a kwanan nan. Lamarin ya ja ra'ayin masana da masu sharhi na ta tofa albarkacin bakinsu kan batun. Wannan ya sa jaridar Tantabara News ta yi tsokaci akan yadda masana da tarihi ya hango makomar irin wadannan mutane.
A ranar larabar makon jiya ne gwamnatin jahar Kano ta dauki matakin rufe masallacin da malamin ke da'awa da aka fi sani da suna As-habul Kahf da ke takiyar birnin Kano. Haka ma gwamnatin ta hana ma sa yin da'awar tare da yi ma sa wani abu mai kama da daurin talala; da ta bayyana da cewa kandagarki ne ga irin matakan da aka lura ya na dauka na hargitsa jama'a tare da boyayyar manufa mai jirwaye kama da wanka.
  Wanene Abduljabbar Nasir Kabara?
 Abduljabbari dai matashin malami ne mai dimbin magoya baya, mai son daukaka da suna a kafofin sada zumunta na zamani da kafar sadarwa ta YouTube mai kare mashabar Shi'a akaikaice ta karkashin inuwar darikar Kadiriyya.
Mahaifinsa, Shaikh Nasiru Kabara, wanda shi ne jagoran darikar Kadiriyya a Kano da yayi suna a lokacinsa, ko da ya ke shi ma ya samu takon saka da wasu malamai ma su neman a hargitsa, irin su Sheikh Bala Kalarawi Kano. An dai bayyana mahaifin Abduljabbari a matsayin mutum mai bambancin ra'ayi da saukin kai ba irin yadda shi dansa ya ke ba.
Me Ya Jawo Aka Dakatar Da Shi Wa'azi?
To amma kuma, wannan matakin da gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya dauka, a ganin wasu bai rasa nasaba da siyasa; wasu kuma na ganin kin darikar ne.
A ra'ayin Muhammad Sidk Qaddam Isah mazauni Hadaddiyar Daular Larabawa, kuma mai sharhi akan al'amurran gabas ta tsakiya da ma sauran duniya, ba haka ba ne. Ya kalli wannan mataki a matsayi kyakkyawa, a bisa hujjojin da ya za zayyano a mukalar da ya wallafa a shafinsa na bulog, a harshen turanci da yayi ma take: Kano Kogo Cleric, wato Malamin Kogo na Jahar Kano. Kogo anan ya samo asali ne daga sunan masallacinsa, As-habul Kahf wanda ke nufin mutanen kogo.
Muhammad Qaddam ya kara da cewa, "Malamin mai karancin haddar Al-kur'ani da karancin ilmin tajwidinsa.....na kokarin kawo ko-kwanto ga hadisan manzon tsira tare da kokarin fassara hadisan ta gundarin zahirinsu a maimakon sakonsu. Yana amfani da gurgun ilmin harshen larabcin da ke da kasawa, wajen bayyana ma'anar (hadisan) da za ta kai ga karshe ya karyata su, ya watsar da su".
"Ya kan bin salon Mu'utizilawa masu akidar Shi'a da ke suka ga hadisai tare da bayyana raddin da ba a gina ga hujja ba. A maimakon (tsarin da aka sani) shi ya kan ce fassarar da yayi mu su a bisa ra'ayinsa ne da ilminsa ya ke kawo tartibin yadda sahabbai da na bayansu suka bayyana addinin musulunci a daruruwan shekaru".
     (mohammadsidq.blogspot.com
Haka ma jaridar Daily Trust ta ranar Jumu'a 5/2/2021 ta buga sharhin).
Gwamna Ganduje dai ya bayyana dalilin cewa akwai alamar Abduljabbari na kira ne da a yi tawaye, da kisan kai da nuna kangara wa gwamnati a dukan wa'azojinsa. Misalin hakan shi ne wani kira da ya ke na cewa duk wanda ya shiga wajen da ya ke wa'azi don ya farma (kama) sa, to magoya bayansa su "kama wannan mutumin su yanka shi, su yanka shi, su yanka shi"!!
Wanda a cewar gwamnati yana nufin jami'a tsaro.
Ganduje ya bayyana hakan a kafafen watsa labarai cewa, bai dauki matakin dakatar da shi daga wa'azi tare da rufe masallacin haka siddam ba, sai da ya samu rahotanni da shawarwari daga muhimman mutane.
Wasu na ganin akwai siyasa a ciki lura da yadda dangantaka ta yi tsami tsakanin gwamna Abdullahi Umar Ganduje da tubabben sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II, wanda shi sarkin Kanon na goyon bayan gidan su marigayi Nasiru Kabara, in da nan ne Abduljabbari ya fito.
Galibin jama'a na ganin daukan matakin ya dace, ganin irin yadda a hakan Maitatsine ya fara a Kanon; haka shugaban kungoliyar Boko Haram na farko Muhammad Yusuf ya fara. Kuma shi ma Muhammad Yusuf yayi zaman mukabila da manyan malamai irin su marigayi Shaik Jafar Adam Kano da marigayi Shaik Albani Zariya da Shaik Isah Ali Pantami da sauran su, akan cewa da'awar da ya ke ta sabawa shari'a wanda sai yanzu ne jama'a suka gasgata su alhali an makara.
A kan wannan aka bayyana Abduljabbari Nasir Kabara a matsayin mai neman suna da son mamaye manyan malaman hadisi ta hanyar tara magoya baya da karkatar da su don neman dagawa a sama.
Sai dai a ra'ayin magoya bayansa, shi mutim ne da ya zo da niyyar tsarkake tsarin koyarwar addini da yadda ake wa'azi ana jingina wasu hadisai ga annabi mai tsira da amincin Allah.
Wani abu da ake danganta Abduljabbar da shi, bai wuce goyon bayan akidar Shi'a a kaikaice ba. Shi da kan sa ya karyata hakan amma ya bayyana cewa ya "rantse da Allah ko a haka Shi'a ta fi sunna sau dari", sai dai bai bayyana wace sunnar ba.
A wasu daga bidiyoyinsa ya taba cewa ko da Ganduje ya aiko a kashe shi, a harbe shi to ba shi aka haifa ba "Annabi (S.A.W.) aka harba!!!" Irin wadannan magangannu sun jawo an kasa gane in da ya dosa, kuma mutane hatta magoya bayan darkar ta Tijjaniya suka soma tunanin ta natsu da zargin lamarin kama da tauraruwa mai wutsiya, da ma su iya magana suka ce ganin ta ba alhairi ba!.
Koma dai menene, lokaci zai tabbatar da shi. Kamar yadda wasu ke cewa da wuya gwamna Ganduje bai kare da shi ba, kamar yadda gwamnan jahar Kaduna Malam Nasir El-Rufa'i ya kare da Elzakzaki.
WANNAN RA'AYI NE NA JARIDAR TANTABARA NEWS, KUMA BAI DA MANUFAR SUKA KO BATANCI GA KOWA.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Stepping Down Not The Right Option - Osinbajo

Vice president Yemi Osinbajo has denied reports that he intends to step down for a certain presidential aspirant ahead of the presidential primary of the All Progressives Congress (APC). The denial is contained in a statement by the chairman of Osinbajo’s campaign council, Richard Akinnola on Sunday. According to the statement, the people behind the speculation are “afraid of the huge political support base of the Vice President, Prof. Yemi Osinbajo,” adding that the VP is ready for the presidential primary scheduled to hold between June 6 and 8. The campaign council “welcomes our distinguished delegates from across the country to Abuja for our presidential primaries. “As you settle down in Abuja, we implore you to kindly disregard various fake news making the rounds that Prof. Yemi Osinbajo has stepped down. “Osinbajo would be hoping to clinch the ticket of the ruling party with much desire to take over from his principal, President Muhammadu Buhari at the end of his tenur...

An Sako Ƙarin Fasinjojin Jirgin Ƙasa Bakwai Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Wasu fasinjoji bakwai da aka yi garkuwa da su a harin jirgin kasa na ranar 28 ga Maris a jihar Kaduna sun samu 'yanci. An sako mutanen ne a safiyar Laraba bayan sun shafe kwanaki 135 a hannun ‘yan ta’addan. Sai dai ba a bayyana ko an biya kudin fansa ga 'yan ta'addar domin a sako su ba. Ɗaya daga waɗanda suka shiga sasantawar mai suna Tukur Mamu, ya fada  a wata sanarwa a ranar Laraba cewa shida daga cikin wadanda aka sako ‘yan gida daya ne, wadanda suka hada da ma’aurata da ‘ya’yansu hudu.  Sanarwar ta ce an sako yaran da iyayensu ne bayan da Sheik Ahmad Gumi ya shiga tsakani

92 Feared Dead As Oil Tanker Explodes in Sierra Leone

A huge oil tanker explodes in Sierra Leone's capital;  more than 90 people are feared dead.  Many people were injured, and most were seriously injured.  Local reports say Freetown hospitals are overcrowded.  The bomber struck shortly after noon in front of a petrol tanker.  Pictures posted on social media showed the blaze burning at the scene as the fuel spread, with several cars burning and causing an explosion.  The chairman of the National Emergency Management Agency, Lieutenant-General Brima Sesay, described the situation as "extremely serious" and said the bodies had been burnt. Bashir Ahmad Zubairu is a multi-media journalist in Nigeria Email: bashir.visionfmradio@gmail.com

We Are Not Exceptional - Zamfara State Legislators

The Zamfara state government has taken a stand against President Muhammadu Buhari's order to ban all flights across the state. State legislators voted against the move, describing it as action speaks louder than words. One of the law makers in the state who came up with the bill, Faruku Dosara, slammed the federal government and retaliated against President Buhari's security adviser, retired Major General Babagana Munguno, for his alleged negligence in the issues concerning security and prosecuting suspects involved in the case. About 300 Jangebe Science Secondary School students were recently abducted and held captive by gunmen for several days before being released, which experts say a ransom must be paid before a deal can be reached. Faruku Dosara said, "It is not only Zamfara State that has the issue of kidnapping in Nigeria, there are Dabchi, Kangara, Chibok and Kagara in Niger State. Why is Zamfara different? We are not exceptional". In a...

Why are Arab countries worried about the possible collapse of Iran’s government?

After tensions flared between Washington and Tehran following the Iranian government’s brutal crackdown on protesters, Saudi Arabia, Qatar, and Oman launched a major effort to prevent U.S. President Donald Trump from attacking Iran, out of fear that such a move would trigger a “devastating reaction in the region,” a senior Saudi official told AFP. The Saudi official said the three Gulf countries carried out intense diplomatic efforts to persuade the U.S. president to give Iran’s leaders an opportunity to show remorse, adding that communication channels remain open to help build mutual trust. How do the Persian Gulf countries view their “neighbor plagued by instability,” and what are their concerns about its current situation? Gulf diplomacy in a critical moment. The possibility of U.S. military action against Iran has been a key issue causing serious concern in Arab diplomatic efforts, especially among countries of the Gulf region. This concern stems from their proximity to...

Hukumar Hana Fasa Kwabri Ta Najeriya Ta Kama Buhunan Naman Jaki 1,339

Hukumar ta bayyana kama wannan adadin buhunan naman jaki ne a jahar Kabi da ke arewa maso yammacin Najeriya da aka kiyasta kudinsu ya haura naira miliyan 40. Shuguban hukumar ta kastam Joseph Attah ya ce sun yi nasarar kama kyafaffen naman jakin ne da aka shirya fita da shi. A cewar sa wadanda aka kama da naman sun bayyanawa hukumar cewa fiye da jakuna dubu daya suka yanka kafin su tara wannan adadi. Gwamnatin Najeriya dai ta haramta safarar jakuna zuwa kasashen ketare musamman kasar Sin, wadda ke sahun gaba wajen sayen jakuna a kasashen Afirka da suka hada da Najeriya da Nijar da Mali da Sudan da sauran su. A halin da ake ciki yanzu haka jakuna na barazanar karewa a duniya sakamakon yawan safarar su da ake tare da sarrafa nama da fatarsu ta wasu hanyoyi na daban. Hasalima dai, jaki dabba ce da kan hai fi da daya kwal a cikin shekaru ba kamar sauran dabbobi ba da ke haihuwa biyu zuwa uku a shekara.

'Yan Bindiga Sun Kai Hari Gidajen Ma'aikatan Filayen Jiragen Saman Najeria Tare Da Sace Mutum 11

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kai hari a gidajen ma'aikatan Hukumar Filin Jirgin Saman Tarayyar Najeriya da ke Kaduna, inda suka yi awon gaba da akalla mutane 11. Rahotannin baya-bayan nan sun kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi nasarar sace ma’aikacin Hukumar Kula da Sararin Samaniyar Najeriya (NAMA)A, da matarsa, da jami’in Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NIMET) da ya’yansa, kuma har yanzu ba a san inda suke ba. Satar mutane ya zama ruwan dare a Najeriya a yau, kuma kusan kowace safiya ana samun rahotannin kashe-kashe ko satar mutane don neman kudin fansa.  A makon da ya gabata ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sha alwashin kawo karshen satar mutane a Najeriya amma ga dukkan alamu kalaman nasa ba su yi tasiri ba. 

Gunmen Killed Suswam Elder Brother

Gunmen in a car have killed Terkula Suswam, the elder brother of former Benue State Governor Gabriel Suswam. They also killed his aide in an attack that occurred at Anyiin in Gaambetiev of Logo Local Government Area at about 8.40 pm in the late evening. An eyewitness said he was working outside his compound when a Toyota car, speedily approached him. The source said the victim suspected the vehicle’s occupants to be gunmen and attempt to run into the compound before he was shot. Recent attacks and kidnapping in Nigeria lead thousand of people to leave their homes and instead end up as refugees in other places and this stuation put many in dillema.