Skip to main content

TAURARUWA MAI WUTSIYA... GANDUJE KO ABDULJABBARI?

RA'AYI:
Dambarwar da ta dabaibaye batun nan na dakatar da Abduljabbar Nasiru Kabara a jahar Kano na ta jan hankalin al'umma a kwanan nan. Lamarin ya ja ra'ayin masana da masu sharhi na ta tofa albarkacin bakinsu kan batun. Wannan ya sa jaridar Tantabara News ta yi tsokaci akan yadda masana da tarihi ya hango makomar irin wadannan mutane.
A ranar larabar makon jiya ne gwamnatin jahar Kano ta dauki matakin rufe masallacin da malamin ke da'awa da aka fi sani da suna As-habul Kahf da ke takiyar birnin Kano. Haka ma gwamnatin ta hana ma sa yin da'awar tare da yi ma sa wani abu mai kama da daurin talala; da ta bayyana da cewa kandagarki ne ga irin matakan da aka lura ya na dauka na hargitsa jama'a tare da boyayyar manufa mai jirwaye kama da wanka.
  Wanene Abduljabbar Nasir Kabara?
 Abduljabbari dai matashin malami ne mai dimbin magoya baya, mai son daukaka da suna a kafofin sada zumunta na zamani da kafar sadarwa ta YouTube mai kare mashabar Shi'a akaikaice ta karkashin inuwar darikar Kadiriyya.
Mahaifinsa, Shaikh Nasiru Kabara, wanda shi ne jagoran darikar Kadiriyya a Kano da yayi suna a lokacinsa, ko da ya ke shi ma ya samu takon saka da wasu malamai ma su neman a hargitsa, irin su Sheikh Bala Kalarawi Kano. An dai bayyana mahaifin Abduljabbari a matsayin mutum mai bambancin ra'ayi da saukin kai ba irin yadda shi dansa ya ke ba.
Me Ya Jawo Aka Dakatar Da Shi Wa'azi?
To amma kuma, wannan matakin da gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya dauka, a ganin wasu bai rasa nasaba da siyasa; wasu kuma na ganin kin darikar ne.
A ra'ayin Muhammad Sidk Qaddam Isah mazauni Hadaddiyar Daular Larabawa, kuma mai sharhi akan al'amurran gabas ta tsakiya da ma sauran duniya, ba haka ba ne. Ya kalli wannan mataki a matsayi kyakkyawa, a bisa hujjojin da ya za zayyano a mukalar da ya wallafa a shafinsa na bulog, a harshen turanci da yayi ma take: Kano Kogo Cleric, wato Malamin Kogo na Jahar Kano. Kogo anan ya samo asali ne daga sunan masallacinsa, As-habul Kahf wanda ke nufin mutanen kogo.
Muhammad Qaddam ya kara da cewa, "Malamin mai karancin haddar Al-kur'ani da karancin ilmin tajwidinsa.....na kokarin kawo ko-kwanto ga hadisan manzon tsira tare da kokarin fassara hadisan ta gundarin zahirinsu a maimakon sakonsu. Yana amfani da gurgun ilmin harshen larabcin da ke da kasawa, wajen bayyana ma'anar (hadisan) da za ta kai ga karshe ya karyata su, ya watsar da su".
"Ya kan bin salon Mu'utizilawa masu akidar Shi'a da ke suka ga hadisai tare da bayyana raddin da ba a gina ga hujja ba. A maimakon (tsarin da aka sani) shi ya kan ce fassarar da yayi mu su a bisa ra'ayinsa ne da ilminsa ya ke kawo tartibin yadda sahabbai da na bayansu suka bayyana addinin musulunci a daruruwan shekaru".
     (mohammadsidq.blogspot.com
Haka ma jaridar Daily Trust ta ranar Jumu'a 5/2/2021 ta buga sharhin).
Gwamna Ganduje dai ya bayyana dalilin cewa akwai alamar Abduljabbari na kira ne da a yi tawaye, da kisan kai da nuna kangara wa gwamnati a dukan wa'azojinsa. Misalin hakan shi ne wani kira da ya ke na cewa duk wanda ya shiga wajen da ya ke wa'azi don ya farma (kama) sa, to magoya bayansa su "kama wannan mutumin su yanka shi, su yanka shi, su yanka shi"!!
Wanda a cewar gwamnati yana nufin jami'a tsaro.
Ganduje ya bayyana hakan a kafafen watsa labarai cewa, bai dauki matakin dakatar da shi daga wa'azi tare da rufe masallacin haka siddam ba, sai da ya samu rahotanni da shawarwari daga muhimman mutane.
Wasu na ganin akwai siyasa a ciki lura da yadda dangantaka ta yi tsami tsakanin gwamna Abdullahi Umar Ganduje da tubabben sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II, wanda shi sarkin Kanon na goyon bayan gidan su marigayi Nasiru Kabara, in da nan ne Abduljabbari ya fito.
Galibin jama'a na ganin daukan matakin ya dace, ganin irin yadda a hakan Maitatsine ya fara a Kanon; haka shugaban kungoliyar Boko Haram na farko Muhammad Yusuf ya fara. Kuma shi ma Muhammad Yusuf yayi zaman mukabila da manyan malamai irin su marigayi Shaik Jafar Adam Kano da marigayi Shaik Albani Zariya da Shaik Isah Ali Pantami da sauran su, akan cewa da'awar da ya ke ta sabawa shari'a wanda sai yanzu ne jama'a suka gasgata su alhali an makara.
A kan wannan aka bayyana Abduljabbari Nasir Kabara a matsayin mai neman suna da son mamaye manyan malaman hadisi ta hanyar tara magoya baya da karkatar da su don neman dagawa a sama.
Sai dai a ra'ayin magoya bayansa, shi mutim ne da ya zo da niyyar tsarkake tsarin koyarwar addini da yadda ake wa'azi ana jingina wasu hadisai ga annabi mai tsira da amincin Allah.
Wani abu da ake danganta Abduljabbar da shi, bai wuce goyon bayan akidar Shi'a a kaikaice ba. Shi da kan sa ya karyata hakan amma ya bayyana cewa ya "rantse da Allah ko a haka Shi'a ta fi sunna sau dari", sai dai bai bayyana wace sunnar ba.
A wasu daga bidiyoyinsa ya taba cewa ko da Ganduje ya aiko a kashe shi, a harbe shi to ba shi aka haifa ba "Annabi (S.A.W.) aka harba!!!" Irin wadannan magangannu sun jawo an kasa gane in da ya dosa, kuma mutane hatta magoya bayan darkar ta Tijjaniya suka soma tunanin ta natsu da zargin lamarin kama da tauraruwa mai wutsiya, da ma su iya magana suka ce ganin ta ba alhairi ba!.
Koma dai menene, lokaci zai tabbatar da shi. Kamar yadda wasu ke cewa da wuya gwamna Ganduje bai kare da shi ba, kamar yadda gwamnan jahar Kaduna Malam Nasir El-Rufa'i ya kare da Elzakzaki.
WANNAN RA'AYI NE NA JARIDAR TANTABARA NEWS, KUMA BAI DA MANUFAR SUKA KO BATANCI GA KOWA.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Wata Mota Cike Da Harsasan Bindiga Ta Fada Rami A Garin Awka Na Jahar Imo

Hankalin jama'a yayi matukar tashi a jiya Lahadi biyo bayan gano wata babbar mota cike da harsasai masu rai a birnin Anacha na jahar Imo da ke kudu maso gabashin tarayyar Najeriya. Rahotannin da suka shigo muna na cewa jami'an tsaron cikin hanzari sun afkawa garin na kasuwanci domin daukar matakin gaggawa kan lamarin.  Babbar motar wadda ke dauke da kwaliyoyin harsasai masu rai ta fada cikin wani rami da ke kan titi, inda dukan harsasan suka zube. Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce: “Motar ta fadi, kuma duk titin na cike da harsasai.  Wasu yaran ma sun debi wasu da hannayensu suka gudu, kafin jami’an tsaro su iso wurin. ”  Majiyar ta ci gaba da bayyana cewa direban babbar motar da mai yi masa hidima sun yi watsi da motar bayan hatsarin ya faru, inda suka yi batan dabo zuwa inda ba a sani ba. Amma wata majiyar ta ce ‘yan sanda sun cafke direban. “Lamarin ya jawo jami'an tsaro masu yawa zuwa yankin hanyar Awka da da safiyar yau. 'Yan sanda sun...

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

An Ruguza Makarantar Malam Abduljabbar Kano

Dazu dazun nan gwamnatin jahar Kanon ta tura jami'an ma'aikatar lura da tsarin filaye in da ta ruguza makarantar Malam Abduljabbar. Gwamnatin dai ta taba bayyana cewa filin da ya ke amfani da shi haramtacce ne, in da ta kai ga kwace shi tare da bada umurnin gudanar da wasu muhimman ayukka a wurin. Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin gwamnatin jahar Kano da Abduljabbar in da a ranar laraba sakataren watsa labaran gwamnatin jahar, Muhammad Garba ya bayar da sanarwar rufe masallacin Malam Abduljabbar tare da hana masa gudanar da wa'azi baki daya. In da ta ce hakan na da alaka da irin yadda ya ke tunzura jama'a a kalaman da ya ke amfani da su a lokacin da ya ke da'awa.

Gunmen Abducted 11 FAAN Staff In Kaduna

A group of gunmen yesterday attacked the residences of the Federal Airport Authority of Nigeria Kaduna. Reports say gunmen stormed the compound and abducted at least 11 people. Recent reports suggest that the bandits also abducted a staff of  Nigerian Airspace Management Agency NAMA, his wife, a National Meteorological Agency (NIMET) official and his children.Their whereabouts are still unknown. Kidnappings are common in Nigeria today, and almost every morning there are reports of killings or kidnappings for ransom. Last week Nigerian President Muhammadu Buhari vowed to end abduction in Nigeria but for all indications his words were not effective.

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."

Burtaniya Ta Kakabawa Bankunan Rasha da Mahukuntan Kasar Takunkumin Tattalin Arziki Mafi Girma A Tarihi

Getty images Firaministan Burtaniya, Boris Johnson ya sanar da sakawa Rasha takunkumi mafi tsanani a bangaren tattalin arziki da Rasha ta taba gani, tun bayan da ta mamaye Ukraine. Da yake magana a zauren majalisar, firaministan ya ce za a daskarar da duk wasu manyan bankunan kasar Rasha da kuma cire su daga tsarin kudi na Burtaniya.  Har ila yau, za a dakatar da kamfanin jiragen saman Rasha na Aeroflot sauka a kasar Birtaniya. Mista Johnson ya shaidawa majalisar dokokin kasar a yammacin ranar almais din makon nan cewa, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin "mai cin zali ne mai zubar da jini, don haka zai yabawa aya zakinta".

Yahaya Bello Ya Caccaki Buhari

Da ya ke jawabi a lokacin da ake gudanar da shirin zaben fitar da gwani, gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello ya nemi a zabe shi domin ya magance matsalar tsaro da karancin ilmi da ake fama da su yanzu haka a Najeriya. Ya ce, "akwai takaici ace wai yanzu malaman jami'a suna ci gaba da yajin aiki, dalibai na zaune a gida kuma an kasa magance wannan matsala mai saukin magancewa". Yahaya Bello wanda ya ce ba zai jaye ma kowa a neman tikitin shugaban kasa, ya kara da cewa shi matashi ne kuma matasa ya kamata a ba dama su mulki kasar nan ba tsofaffi da suka gaji ba. Ya yabawa shugaba Buhari akan saka hannu a kan dokar ba matasa damar tsayawa takara, in da ya ce abu ne mai kyau. Ya yi kira ga mata da sauran 'yan Najeriya da ya ce ana zalunta da su zabe shi. Dan takarar ya ce "yanzu haka babu tsaro ko kadan kuma an kyale, ana kashe mutane ana kona mu su dukiya kuma ana kallo an zura ido".

Binani Ta Zama Mace Ta Farko Da AKa Zaɓa Gwamna A Najeriya

A wani abinda ba saban ba, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Sanata Aisha Dahiru, wacce aka fi sani da Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen gwamnan jahar Adamawa. Kwamishinan zaɓen jahar Adamawa, Farfesa Hudu Yunus Ari, ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ana tsakiyar tattara sakamakon zaɓen. An bayyana sakamako daga ƙananan hukumomi 10 cikin 20 yayin da aka dage ci gaba da bayyana sakamakon zaɓen har zuwa karfe 11 na safe. Sai dai Ari ya sanar da sakamakon ƙarshe awa ɗaya kafin lokacin da aka tsara. Gwamnan jahar Ahmadu Fintiri na jam'iyyar PDP ne ke kan gaba kafin a bayyana hakan. Wasu magoya bayan jam’iyyar PDP a zauren sun nuna rashin amincewarsu da dalilin da ya sa kwamishinan zaɓe ya sanar da sakamakon maimakon baturen tattara sakamakon zaɓe a al'adance.