Skip to main content

Sabuwar Kwayar Cutar Korona Ta Soma Yaduwa

A farkon makon nan a ka gano wata nau'in kwayar cutar korona da ta sha bamban da wacce aka sani.
Ita dai wannan sabuwar kwayar cuta ta bulla ne a kasar Burtaniya, in da ta yi nasarar mamaye birnin Landan da gasbascin kasar a yankunan Surrey, Essex, Backshire, Backinghamshire Kent da sauran su.
Firaminstan kasar Boris Johnson ya ce a halin da ake ciki yanzu, kwayar cutar na bazuwa ne cikin sauri fiye da ta farko; wanda yanzu haka ta ke kashi 70 cikin dari a mizanin yaduwa.
Masana kiyon lafiya a duniya sun bayyana cewa, ba Burtaniya kadai wannan sabuwar korona ta bulla ba, har da da Afirka ta kudu da ma sauran sassan duniya kawai dai ba a kai ga farga da hakan ba ne. A cewar su, Burtaniya dai ce ta yi kwakkafin gano ta saboda tsananin bincike da gwajin da ta fi kowace kasa yi kan wannan cuta.
Tuni dai kasashen duniya da suka hada da Jamus, Faransa, Italiya, Austireliya, Iceland, Spaniya, Saudiyya da sauran su, suka dakatar da zirga zirgar jiragen sama tsakaninsu da kasar ta Burtaniya.
Annobar korona dai ta sake dawowa da wata fuska ta daban, in da ko a karshen makon jiya kimanin mutum 27,000 suka kamu da ita a Amurka a rana daya kawai.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey