Skip to main content

Sabuwar Kwayar Cutar Korona Ta Soma Yaduwa

A farkon makon nan a ka gano wata nau'in kwayar cutar korona da ta sha bamban da wacce aka sani.
Ita dai wannan sabuwar kwayar cuta ta bulla ne a kasar Burtaniya, in da ta yi nasarar mamaye birnin Landan da gasbascin kasar a yankunan Surrey, Essex, Backshire, Backinghamshire Kent da sauran su.
Firaminstan kasar Boris Johnson ya ce a halin da ake ciki yanzu, kwayar cutar na bazuwa ne cikin sauri fiye da ta farko; wanda yanzu haka ta ke kashi 70 cikin dari a mizanin yaduwa.
Masana kiyon lafiya a duniya sun bayyana cewa, ba Burtaniya kadai wannan sabuwar korona ta bulla ba, har da da Afirka ta kudu da ma sauran sassan duniya kawai dai ba a kai ga farga da hakan ba ne. A cewar su, Burtaniya dai ce ta yi kwakkafin gano ta saboda tsananin bincike da gwajin da ta fi kowace kasa yi kan wannan cuta.
Tuni dai kasashen duniya da suka hada da Jamus, Faransa, Italiya, Austireliya, Iceland, Spaniya, Saudiyya da sauran su, suka dakatar da zirga zirgar jiragen sama tsakaninsu da kasar ta Burtaniya.
Annobar korona dai ta sake dawowa da wata fuska ta daban, in da ko a karshen makon jiya kimanin mutum 27,000 suka kamu da ita a Amurka a rana daya kawai.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Wanene Ɗan Jarida?

Ɗan jarida mutum ne kamar kowa, sai dai tunaninsa da manufofinsa kan tafi daidai ne kawai da ra'ayin MASU SAURARO ta fuskokin da suka shafi aikinsa. Ya zama mai wakiltar waɗanda ba su da baki ne ko kafafuwan zuwa, kuma idanuwan talakawa a kowane lokaci. Idan ka nuna ma sa launi shuɗi, ƙoƙarin ya ke ya tabbatar da launin nan shuɗi ne ziryan ko yana da garwaye? Idan ka ce ma sa labarin abu kaza ya faru, ba zai ce a'a ba kuma ba zai ce eh ba, aikinsa shi ne TABBATARWA . Idan mai sauraro namiji ne ko mace ko mai ra'ayin wani addini ko akida ko mai kuɗi ko talaka, ɗan jarida kan GIRMAMA kowa, kuma zai ɗauki kowa a matsayin DAIDAI ta fuskar ba su damar bayyana ra'ayoyinsu. Ɗan jarida kan tafi da zamani, ya kuma rungumi fasahar da ƘIRƘIRA ta kawo domin tafiya daidai lokaci. A kowace marra GASKIYA ita ce madogarar ɗan jarida, kuma wannan kan ƙara sa masu sauraro su amince da shi. Amma kuma, dole ne ɗan jarida ya zama MAI IKON KANSA , ba zai yi ma kowa alfarma b...

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...