Skip to main content

Farkawar Matan Afirka

Afirka nahiya ce mai dogon tarihi. Tun asali,  yawancin Turawa sun yi kokarin sanya idanu a kan nahiyar, sun ziyarce ta don neman ko dai kasuwanci, wanda a wancan lokacin wani nau'i ne na cinikin bayi ko kuma daga baya ya koma ga cinikin kayan masarufi kamar su gyada, auduga, fatun dabbobi da makamantansu.
Zuwan Larabawa kuma, a wasu lardunan Afirka na lokacin, gami da yankin da ake kira "Sudaniyya", wanda ya hada da Sudan, Najeriya, Chadi, da wasu sassan Jamhuriyar Nijar, ya haifar da yaduwar Musulunci da al'adun Gabas.Daga baya, zuwan Bature ya kawo kiristanci, ilimin yamma da sauran manufofin Turawa.Nahiyar Afirka sannu a hankali tana juyawa zuwa matakai daban-daban; daga duhun kai har zuwa halin da ake ciki a yau.Ilimin addini da na zamani sun samu gindin zama a kasashen Afirka, amma har yanzu mata suna baya a wannan tafiyar.
Sau da yawa za ka ga mata a yankunan karkara har ma da wasu biranen Afirka cikin yanayin talauci da jahilci ba tare da samun wadataccen ilimi ba.Kowace rana, ana ganin mata dauke da itacen girki, wasu dauke da jarirai a bayansu suna zuwa rafuka ko ma gonaki don noman abinci da za a ci.
A irin wannan tsari mai kama da bauta, akwai kabilu a arewacin Najeriya da kuma kudanci inda matansu ke noma, suna renon yara da kuma dafa abinci a gida.
Hasali ma dai, a kudancin Najeriya, akwai kabilun da ke hana mata gadon iyayensu da suka mutu.
Al'ada da ra'yi na waɗannan kabilun, maza ne kawai da haƙƙin gado har ma da matar mutumin, koda kuwa mamacin mahaifinsa ne.
Wannan halin ya samo asali ne sakamakon rashin ilimin zamani da na addini wanda yawancin mata suke dashi.
A kasashe irin naTurai da Amurka mata suna da 'yanci  da ya yi daidai da al'adunsu da addininsu, kenan abu ne mai kyau idan a Afirka mutane sun rike addininsu tare da kyawawan al'adunsu, kuma su guji nuna bambanci da hadama.
A cikin addini babu wani wuri da ake hana kowace mace gado, sai dai ga kowane addini akwai wani tsari na musamman kuma mabiyansa sun yi imani da shi, kuma ba za su yarda da shisshigi daga wasu ba.

Ba Afirka kawai ake samun irin wannan ba har ma a kasashen Larabawa da na Asiya, inda har yanzu ake tauye ‘yancin mata ta hanyar hana su damar samun ilimi, sana’o’in dogaro da kai har ma da 'yancin auren wanda suke so; maimakon haka, zabin magabatansu shine zabinsu ko suna so ko basa so.
Duk da haka, wannan ɓangaren na matan Afirka a yanzu yana neman taimako ta hanyoyi da yawa, gami da goyon bayan magabatansu kamar iyaye da mazajensu da goyon bayan gwamnatoci har ma shugabannin addinai.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."