Skip to main content

Jam'iyyu 13 Sun Yi Barazanar Ƙauracewa Zaɓe A Najeriya

Gamayyar jam'iyyun adawa 13 sun bayyana cewa za su ƙauracewa shiga zaɓe muddin Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ƙara wa'adin amfani da tsofaffin kuɗaɗe daga lokacin da aka ɗiba tun da farko.
Shugaban jam'iyyar AA Kennetth Udeze ne ya fitar da wannan sanarwa, in da ya ce canjin fasalin kuɗi da CBN ya fito da shi zai haifar da babban tasiri a tattalin arziki da fannin tsaro kana sun kai matsayar watsi da sabon matakin da gwamnonin APC suka ɗauka da suka haɗa da na Kaduna, Malam Nasiru El-rufai da na Zamfara Bello Mutawalle da na Kogi Yahaya Bello, na maka shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a gaban kotu kan sauya takardun kuɗi da ya yi.

A Najeriya akwai jerin jam'iyyu 18 da za su fafata a babban zaɓe mai zuwa sai dai 13 daga ciki sun yi barazanar janye jikinsu daga shiga zaɓen muddin aka ƙara lokacin amfani da tsofaffin kuɗaɗe.

Menene ra'ayinka kan wannan batu?

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey