Skip to main content

Yadda Masu Kuɗi Da Ruwa Suka Cika Harabar ATM

Rahotonni da ke ci gaba da shigo muna yanzu haka, na nuni da cewa ɗaruruwan mutane na ta yi dogayen  layuka a gaban na'urar cirar kuɗi ta ATM da ke bankuna, inda suke amfani da wani salo na biyan mutane domin su ciro mu su kuɗi.
Wani da muka zanta da shi mai suna Lawal Mai Masara, ya shaida muna cewa, tun jiya ya ke kan layi, kuma har yanzu bai kai ga samun kuɗin ba saboda masu sana'ar POS da masu kwashe kuɗi su sake adanawa sun cika ko'ina.
"Za ka ga mutane riƙe da katunan cirar kuɗi fiye da 10 inda suke tura ma wasu kuɗi su rarraba musu katunan domin a cire mu su kuɗin a ATM daga baya su bayar da naira dubu akan duk dubu goma da aka cire mu su". In ji shi.
Mutumin ya ƙara da cewa wannan na daga cikin manyan dalilan da suka haddasa ƙarancin kuɗi tsakanin mutane a Najeriya.musamman arewa.

Wannan sabon matakin ya nuna irin yadda mutane ke jefa kansu a halin tasku ta hanyar ci gaba da kwashe kuɗaɗen da jama'a ya kamata su samu.

Wani ganau da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ya zama wajibi hukumomin tsaro sau ɗauki matakin yi wa tufkar hanci muddin ana son a samu sauƙi a rayuwa.

"Ta ya za a samu sauƙi bayan mutane sun mayar da kansu 'yan-jari-hujja?
Kuma a haka ake neman samun shugabanni na gari bayan kowa ya zama maketacin ɗan'uwansa". In ji shi.

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Turai na fuskantar tsananin zafi

Burtaniya  Wani matsanancin yanayin zafi ya karaɗe yammaci da arewacin Turai, inda yanayin zafi ya zarta yadda aka saba sosai, kuma ya kai yanayin da aka jima ba a gani irinsa ba a ƙasasahe da dama. Birtaniya da Faransa sun fuskanci yanayin zafin da ba su taɓa ganin irinsa ba a watan Mayu, yayin da iska mai huci ta sa zafin ya kai ƙoluwar da ba a saba ganin irinsa ba ko da a lokacin tsanananin zafi.  Paris a Faransa  Jami’an kula da yanayi sun yi gargaɗin cewa yanayin zafin wata alama ce ta ɗumamar duniya.