Skip to main content

An Kashe Ɗan Takarar Jam'iyyar Labour A Kudu Maso Gabas

Ana ci gaba da samun tashe-tashen hankula a yankin Kudu maso Gabas hatta a cikin makon da za a gudanar da babban zaɓen 2023.
Rahotanni daga yankin sun ce wasu da ba gano ba sun kashe Mista Oyibo Chukwu, ɗan takarar ɗan majalisar dattawa mazabar Enugu ta gabas a ranar Asabar, sa’o’i 48 kafin gudanar da zaɓen.
An kashe Chukwu ne tare da wasu magoya bayansa biyar a ƙaramar hukumar Awkunanaw ta Enugu a lokacin da yake dawowa daga wani gangamin yaƙin neman zaɓe.
An kuma ce masu kisan sun kona shi da magoya bayansa bayan sun tare da shi a cikin motarsa.
Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar Labour, Chijioke Edeoga, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce jam’iyyun siyasa na yi wa ‘ya’yan jam’iyyarsa kisan gilla, waɗanda ke ganin barazana ce ga bunƙasar jam’iyyar a jihar.

Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour, ya fito ne daga yankin Kudu maso Gabas, wanda tashin hankali ya zama ruwan dare, tun kafin lokacin zaɓe.

 Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sha alwashin gurgunta zaɓen da ke tafe a yankin amma jami’an tsaro sun tabbatar wa mazauna yankin cewa za su yi duk mai yuwa domin shawo kan lamarin.

Har kawo yanzu dai rundunar ‘yan sandan jihar Enugu ba ta mayar da martani kan lamarin ba, wanda Edeoga ya ce yana da alaƙa da siyasa.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."