Skip to main content

Kalubalen Tsaro Da Canza Shekar Kwamishinan Tsaron Jahar Sokoto

 

A daidai lokacin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a jahar Sokoto, kwamishinan tsaron jahar Kanal Garba Moyi (mai ritaya) ya bayar da sanarwar aje muƙaminsa tare da ficewa daga jam’iyyar jam’iyar PDP mai mulkin jahar.

A cewar tsohon kwamishinan tsaron, “akwai gaggan matsaloli da suka taka rawa wajen ficewarsa daga jam’iyayar, da suka haɗa da sakacin gwamnan jahar, Aminu Waziri Tambuwal na watsi da dukan  shawarwarin da ake ba shi da suka shafi tsaro; kazalika da rashin sauraren ƙorafe- ƙorafen dangane da ci gaban jahar a fannoni da dama”.

A ranar alhamis da ta gabata dai wasu ‘yan bindiga suka kai wani hari a garin Chakai da ke Ƙaramar Hukumar Mulki ta Tambuwal, wadda ita ce mahaifar gwamnan jahar, in da suka sace mutum goma sha bakwai ciki har da mata da ƙananan yara, tare da neman diyyar naira miliyan takwas da dubu ɗari biyar. Kazalika, sun fitar da sanarwar shirin hallaka mutanen daga gobe talata, muddin ‘yan uwan wadanda ake garkuwa da sun ba su aika mu su kuɗin fansar da suka nema tun da farko ba.

Wani mai suna Alhaji Muhammadu Ɗanyaya, da aka sace matarsa da kuma ‘yarsa mai takaba, ya shaidawa Tantabara cewa, suna cikin babban ƙalubalen tsaro kuma babu wata huɓɓasa daga ɓangaren gwamnatin jahar Sokoto wajen kawo ƙarshen matsalar;ga shi  kuma gwamnati ta haramta ayukkan ‘yan sa kai ballantana su ji ƙwarin guiwar kare kan su. Ya kuma bayyana rashin tartibiyar hanyar da za su bi wajen samo kuɗin fansar da mayaƙan suka nema, “a halin da ake ciki yanzu, ba mu da kuɗin da ‘yan bindigar suka nema, amma dai muna nan muna ƙoƙarin ganin mun sai da gona, an sai da shanu da ‘yan awaki, har ma da kaji dai mata na ta ƙoƙari mai kawo taro sisi na yi, a na ta ƙoƙarin yadda za a haɗa kuɗin, kuma ga shi kudin dai sun buwaya; su kuma suna ta cewa ko ta yaya dole sai a biya kuɗin fansar kafin su sako muna mutanenmu ko su hallaka su daga gobe talata”.

Tantabara ta yi ƙoƙarin ji daga bangaren gwamnatin jahar Sokoto kan wannan lamari amma kawo haɗa wannan rahoto babu wani martani daga mahunkutan.

Jahar Sokoto na cikin sahun gaba a jerin jahohin arewa maso yamma da yanzu haka ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga; in da kwanan nan ‘yan ta’adda suka kai farmaki a garuruwan Tureta da Gidan Dilo da ke yankin Nakasari da Illela da kuma garin Tambuwal.

Kodayake wasu na danganta saukar kwamishinan tsaron jahar ta Sokoto  a matsayin siyasa, wasu masana  na ganin lamarin ya bar baya da ƙura, in da su ke ganin wata babbar koma baya ce a daidai lokacin da ake neman yi ma tufka hanci a fannin na tsaro.

 

 

 


Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey