Skip to main content

Kalubalen Tsaro Da Canza Shekar Kwamishinan Tsaron Jahar Sokoto

 

A daidai lokacin da matsalar tsaro ke Æ™ara ta’azzara a jahar Sokoto, kwamishinan tsaron jahar Kanal Garba Moyi (mai ritaya) ya bayar da sanarwar aje muÆ™aminsa tare da ficewa daga jam’iyyar jam’iyar PDP mai mulkin jahar.

A cewar tsohon kwamishinan tsaron, “akwai gaggan matsaloli da suka taka rawa wajen ficewarsa daga jam’iyayar, da suka haÉ—a da sakacin gwamnan jahar, Aminu Waziri Tambuwal na watsi da dukan  shawarwarin da ake ba shi da suka shafi tsaro; kazalika da rashin sauraren Æ™orafe- Æ™orafen dangane da ci gaban jahar a fannoni da dama”.

A ranar alhamis da ta gabata dai wasu ‘yan bindiga suka kai wani hari a garin Chakai da ke Ƙaramar Hukumar Mulki ta Tambuwal, wadda ita ce mahaifar gwamnan jahar, in da suka sace mutum goma sha bakwai ciki har da mata da Æ™ananan yara, tare da neman diyyar naira miliyan takwas da dubu É—ari biyar. Kazalika, sun fitar da sanarwar shirin hallaka mutanen daga gobe talata, muddin ‘yan uwan wadanda ake garkuwa da sun ba su aika mu su kuÉ—in fansar da suka nema tun da farko ba.

Wani mai suna Alhaji Muhammadu ÆŠanyaya, da aka sace matarsa da kuma ‘yarsa mai takaba, ya shaidawa Tantabara cewa, suna cikin babban Æ™alubalen tsaro kuma babu wata huɓɓasa daga É“angaren gwamnatin jahar Sokoto wajen kawo Æ™arshen matsalar;ga shi  kuma gwamnati ta haramta ayukkan ‘yan sa kai ballantana su ji Æ™warin guiwar kare kan su. Ya kuma bayyana rashin tartibiyar hanyar da za su bi wajen samo kuÉ—in fansar da mayaÆ™an suka nema, “a halin da ake ciki yanzu, ba mu da kuÉ—in da ‘yan bindigar suka nema, amma dai muna nan muna Æ™oÆ™arin ganin mun sai da gona, an sai da shanu da ‘yan awaki, har ma da kaji dai mata na ta Æ™oÆ™ari mai kawo taro sisi na yi, a na ta Æ™oÆ™arin yadda za a haÉ—a kuÉ—in, kuma ga shi kudin dai sun buwaya; su kuma suna ta cewa ko ta yaya dole sai a biya kuÉ—in fansar kafin su sako muna mutanenmu ko su hallaka su daga gobe talata”.

Tantabara ta yi ƙoƙarin ji daga bangaren gwamnatin jahar Sokoto kan wannan lamari amma kawo haɗa wannan rahoto babu wani martani daga mahunkutan.

Jahar Sokoto na cikin sahun gaba a jerin jahohin arewa maso yamma da yanzu haka ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga; in da kwanan nan ‘yan ta’adda suka kai farmaki a garuruwan Tureta da Gidan Dilo da ke yankin Nakasari da Illela da kuma garin Tambuwal.

Kodayake wasu na danganta saukar kwamishinan tsaron jahar ta Sokoto  a matsayin siyasa, wasu masana  na ganin lamarin ya bar baya da Æ™ura, in da su ke ganin wata babbar koma baya ce a daidai lokacin da ake neman yi ma tufka hanci a fannin na tsaro.

 

 

 


Comments

Wadanda aka fi karantawa

NDE Commences Sustainable Training and Loan Disbursement To 100 Youths in Sokoto

The National Directorate of Employment (NDE) has commenced Sustainable Agricultural Development Scheme (SADTS) and loand disbursement to 100 youths in Sokoto. Director-General of NDE, Malam Abubakar Fikpo, disclosed this on Tuesday in Sokoto during the orientation of agricultural loans disbursement held at Shamsuddeen Plaza. Fikpo represented by the Sokoto State NDE Coordinator Mrs Eunice J. Danmallam, said beneficiaries are entitled to N100,000 each at 9 per cent interest rate. He said the beneficiaries were captured under the Agricultural Enhancement Scheme (AES) and Community-Based Agricultural Empowerment Scheme (CBAES). He added they were also under Graduate Agricultural Empowerment Scheme (GAES) and Sustainable Agricultural Development and Empowerment Scheme (SADES). Fikpo said that six months moratorium was given after which  beneficiaries were expected to repay the loan in installments over a period of three years. Dan Mallam expressed gr...

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."