A daidai lokacin da
matsalar tsaro ke Ęara
taāazzara a jahar Sokoto, kwamishinan tsaron jahar Kanal Garba Moyi (mai
ritaya) ya bayar da sanarwar aje muĘaminsa tare da ficewa daga jamāiyyar jamāiyar PDP mai mulkin
jahar.
A cewar tsohon
kwamishinan tsaron, āakwai gaggan matsaloli da suka taka rawa wajen ficewarsa
daga jamāiyayar, da suka haÉa
da sakacin gwamnan jahar, Aminu Waziri Tambuwal na watsi da dukan shawarwarin da ake ba shi da suka shafi tsaro;
kazalika da rashin sauraren Ęorafe- Ęorafen dangane da ci gaban
jahar a fannoni da damaā.
A ranar alhamis da ta
gabata dai wasu āyan bindiga suka kai wani hari a garin Chakai da ke Ęaramar Hukumar Mulki ta
Tambuwal, wadda ita ce mahaifar gwamnan jahar, in da suka sace mutum goma sha
bakwai ciki har da mata da Ęananan
yara, tare da neman diyyar naira miliyan takwas da dubu Éari biyar. Kazalika, sun fitar da sanarwar
shirin hallaka mutanen daga gobe talata, muddin āyan uwan wadanda ake garkuwa
da sun ba su aika mu su kuÉin
fansar da suka nema tun da farko ba.
Wani mai suna Alhaji
Muhammadu Ęanyaya, da aka
sace matarsa da kuma āyarsa mai takaba, ya shaidawa Tantabara cewa, suna cikin babban
Ęalubalen tsaro kuma babu
wata huÉÉasa daga Éangaren
gwamnatin jahar Sokoto wajen kawo Ęarshen
matsalar;ga shi kuma gwamnati ta haramta
ayukkan āyan sa kai ballantana su ji Ęwarin guiwar kare kan su. Ya kuma bayyana rashin tartibiyar
hanyar da za su bi wajen samo kuÉin
fansar da mayaĘan suka
nema, āa halin da ake ciki yanzu, ba mu da kuÉin da āyan bindigar suka nema, amma dai muna nan
muna ĘoĘarin ganin mun sai da gona, an
sai da shanu da āyan awaki, har ma da kaji dai mata na ta ĘoĘari mai kawo taro sisi na yi, a na ta ĘoĘarin yadda za a haÉa kuÉin,
kuma ga shi kudin dai sun buwaya; su kuma suna ta cewa ko ta yaya dole sai a biya
kuÉin fansar kafin su
sako muna mutanenmu ko su hallaka su daga gobe talataā.
Tantabara ta yi ĘoĘarin ji daga bangaren gwamnatin jahar Sokoto kan
wannan lamari amma kawo haÉa
wannan rahoto babu wani martani daga mahunkutan.
Jahar Sokoto na cikin
sahun gaba a jerin jahohin arewa maso yamma da yanzu haka ke fuskantar
hare-haren āyan bindiga; in da kwanan nan āyan taāadda suka kai farmaki a
garuruwan Tureta da Gidan Dilo da ke yankin Nakasari da Illela da kuma garin
Tambuwal.
Kodayake wasu na
danganta saukar kwamishinan tsaron jahar ta Sokoto a matsayin siyasa, wasu masana na ganin lamarin ya bar baya da Ęura, in da su ke ganin wata
babbar koma baya ce a daidai lokacin da ake neman yi ma tufka hanci a fannin na
tsaro.
Comments