Skip to main content

Kalubalen Tsaro Da Canza Shekar Kwamishinan Tsaron Jahar Sokoto

 

A daidai lokacin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a jahar Sokoto, kwamishinan tsaron jahar Kanal Garba Moyi (mai ritaya) ya bayar da sanarwar aje muƙaminsa tare da ficewa daga jam’iyyar jam’iyar PDP mai mulkin jahar.

A cewar tsohon kwamishinan tsaron, “akwai gaggan matsaloli da suka taka rawa wajen ficewarsa daga jam’iyayar, da suka haɗa da sakacin gwamnan jahar, Aminu Waziri Tambuwal na watsi da dukan  shawarwarin da ake ba shi da suka shafi tsaro; kazalika da rashin sauraren ƙorafe- ƙorafen dangane da ci gaban jahar a fannoni da dama”.

A ranar alhamis da ta gabata dai wasu ‘yan bindiga suka kai wani hari a garin Chakai da ke Ƙaramar Hukumar Mulki ta Tambuwal, wadda ita ce mahaifar gwamnan jahar, in da suka sace mutum goma sha bakwai ciki har da mata da ƙananan yara, tare da neman diyyar naira miliyan takwas da dubu ɗari biyar. Kazalika, sun fitar da sanarwar shirin hallaka mutanen daga gobe talata, muddin ‘yan uwan wadanda ake garkuwa da sun ba su aika mu su kuɗin fansar da suka nema tun da farko ba.

Wani mai suna Alhaji Muhammadu Ɗanyaya, da aka sace matarsa da kuma ‘yarsa mai takaba, ya shaidawa Tantabara cewa, suna cikin babban ƙalubalen tsaro kuma babu wata huɓɓasa daga ɓangaren gwamnatin jahar Sokoto wajen kawo ƙarshen matsalar;ga shi  kuma gwamnati ta haramta ayukkan ‘yan sa kai ballantana su ji ƙwarin guiwar kare kan su. Ya kuma bayyana rashin tartibiyar hanyar da za su bi wajen samo kuɗin fansar da mayaƙan suka nema, “a halin da ake ciki yanzu, ba mu da kuɗin da ‘yan bindigar suka nema, amma dai muna nan muna ƙoƙarin ganin mun sai da gona, an sai da shanu da ‘yan awaki, har ma da kaji dai mata na ta ƙoƙari mai kawo taro sisi na yi, a na ta ƙoƙarin yadda za a haɗa kuɗin, kuma ga shi kudin dai sun buwaya; su kuma suna ta cewa ko ta yaya dole sai a biya kuɗin fansar kafin su sako muna mutanenmu ko su hallaka su daga gobe talata”.

Tantabara ta yi ƙoƙarin ji daga bangaren gwamnatin jahar Sokoto kan wannan lamari amma kawo haɗa wannan rahoto babu wani martani daga mahunkutan.

Jahar Sokoto na cikin sahun gaba a jerin jahohin arewa maso yamma da yanzu haka ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga; in da kwanan nan ‘yan ta’adda suka kai farmaki a garuruwan Tureta da Gidan Dilo da ke yankin Nakasari da Illela da kuma garin Tambuwal.

Kodayake wasu na danganta saukar kwamishinan tsaron jahar ta Sokoto  a matsayin siyasa, wasu masana  na ganin lamarin ya bar baya da ƙura, in da su ke ganin wata babbar koma baya ce a daidai lokacin da ake neman yi ma tufka hanci a fannin na tsaro.

 

 

 


Comments

Wadanda aka fi karantawa

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...