Skip to main content

Burtaniya Ta Kakabawa Bankunan Rasha da Mahukuntan Kasar Takunkumin Tattalin Arziki Mafi Girma A Tarihi

Getty images
Firaministan Burtaniya, Boris Johnson ya sanar da sakawa Rasha takunkumi mafi tsanani a bangaren tattalin arziki da Rasha ta taba gani, tun bayan da ta mamaye Ukraine. Da yake magana a zauren majalisar, firaministan ya ce za a daskarar da duk wasu manyan bankunan kasar Rasha da kuma cire su daga tsarin kudi na Burtaniya. 
Har ila yau, za a dakatar da kamfanin jiragen saman Rasha na Aeroflot sauka a kasar Birtaniya. Mista Johnson ya shaidawa majalisar dokokin kasar a yammacin ranar almais din makon nan cewa, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin "mai cin zali ne mai zubar da jini, don haka zai yabawa aya zakinta".

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Osinbajo Ya Fito Takarar Shugaban Kasa

A jiya ne mataimakin shugaban Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsaya takarar shugaban kasar Najeriya a 2023. Ya fadi hakan ne a lokacin wani kwarya-kwaryar buda baki da ya halarta tare da wasu gwamnonin jam'iyyar APC da suka hada da na jahar Kebi Abubakar Atiku Bagudo da na Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i da sauran su. A yau litinin dai ne Osinbajo zai sanar da wannan kudiri nasa a dokance, ta wani jawabi da za a yada ta bidiyo. Idan ana iya tunawa dai watanni biyu da suka gabata mataimakin shugaban Najeriyar ya ce ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari wannan manufa tasa. Kafin bayyana wannan bukata, tuni dai wasu suka fito suka bayyana bukatar tsayawa takarar kujerar shugaban kasa karkashin jam'iyyar APC da suka hada da tsohon gwamnan jahar Legas, Bola Ahmed Tinubu da gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello da Rochas Okorocha da kuma kwanan nan ministan suhuri kuma tsohon gwamnan jahar Ribas, Rotimi Amechi da sauran su.