Skip to main content

Maina Ya Kife A Kotu

 Tsohon shugaban kwamitin hana badakala a hukumar fansho ta kasa Abdulrasheed Maina, ya fadi a kotun birnin tarayya a Abuja, daidai lokacin da ake tsaka da yi masa shari'a.

Tsohon shugaban kwamitin dai ana tuhumar sa ne da badakalar da ta danganci batar da kimanin naira biliyan biyu sa'adda da ya ke jagorancin kwamitin. Tun daga lokacin da aka kai shi kotu Maina ya yi batan dabo bayan da ya samu beli.

Bayan kwashe tsawon lokaci ana neman sa daga bisa ni an yi nasarar gano shi a kasar Jamhuriyar Nijar.

Wannan al'adar faduwa a gaban kwamitocin bincike ba bakuwa ba ce a Najeriya, in da ko watannin baya shugaban kwamitin Hukumar Raya Yankin Naija Delta (NDDC) farfesa Podei ya yi zaman tsumma a kwando, lokacin da yake amsa bahasi a gaban kwamitin majalisar wakilai na kasa dangane da badakalar da ake zargin sa da hannu na karkata kwangiloli da kudaden hukumar zuwa wata hanya daban.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Wanene Ɗan Jarida?

Ɗan jarida mutum ne kamar kowa, sai dai tunaninsa da manufofinsa kan tafi daidai ne kawai da ra'ayin MASU SAURARO ta fuskokin da suka shafi aikinsa. Ya zama mai wakiltar waɗanda ba su da baki ne ko kafafuwan zuwa, kuma idanuwan talakawa a kowane lokaci. Idan ka nuna ma sa launi shuɗi, ƙoƙarin ya ke ya tabbatar da launin nan shuɗi ne ziryan ko yana da garwaye? Idan ka ce ma sa labarin abu kaza ya faru, ba zai ce a'a ba kuma ba zai ce eh ba, aikinsa shi ne TABBATARWA . Idan mai sauraro namiji ne ko mace ko mai ra'ayin wani addini ko akida ko mai kuɗi ko talaka, ɗan jarida kan GIRMAMA kowa, kuma zai ɗauki kowa a matsayin DAIDAI ta fuskar ba su damar bayyana ra'ayoyinsu. Ɗan jarida kan tafi da zamani, ya kuma rungumi fasahar da ƘIRƘIRA ta kawo domin tafiya daidai lokaci. A kowace marra GASKIYA ita ce madogarar ɗan jarida, kuma wannan kan ƙara sa masu sauraro su amince da shi. Amma kuma, dole ne ɗan jarida ya zama MAI IKON KANSA , ba zai yi ma kowa alfarma b...