Skip to main content

Mutum 64 Sun Kamu Da Korona A Kaduna - El-Rufa'i

Gwamnatin jahar Kaduna ta fitar da sanarwar cewa annobar korona ta sake dawowa a jahar.
Gwamnatin jahar ta tabbara da samun sabbin kamuwa da cutar har mutum 64, wanda a cewar ta tuni su ma a ka kebe su.
An kuma jiyo gwamnan jahar Malam Nasiru El-Rufa'i, na cewa muddin jama'ar jahar suka ci gaba da yin biris da dokokin da aka shata musu to babu makawa gwamnatin za ta sake kulle su ruf har sai lokacin da annobar Covid-19 din ta lafa.
Gwamnan ya ce yana mamakin yadda al'umma ke watsi da ka'idojin da tuni aka san da su, na rage cin koso da sanya takunkumi da kuma yawaita wanke hannuwa.
Jahar Kaduna na cikin jahohin da suka fuskanci dokar kulle sakamkon barkewar annobar ta korona a watannin baya.
To sai dai wannan gargadi na gwamnatin jahar ya gamu da suka, musamman ga wadanda ke kallon kalaman a matsayin na 'yan boko.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey