Skip to main content

"Ba Zan Taba Sulhu Da 'Yan Ta'adda Ba" - In ji El-Rufa'i

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Tufa'i ya ce ba zai taba yin sulhu da 'yan bindigar da suka sace dalibai 39 a jihar Kaduna ba.
Ya ce, "ta yaya za ka dauki kudi ka ba dan ta'addan da zai yi amfani da shi ya sayi makamai wanda zai yi amfani da shi a kan ka".

A makon da ya gabata, ‘yan ta’adda sun sace dalibai 39 tare da neman kudin fansa har Naira miliyan 500 daga Gwamnatin Kaduna.
Gwamnan ya fada a watan jiya cewa ba zai taba yin sulhu da duk wani dan fashi da makami don neman kudin fansa ba.
Jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya na fuskantar yawan sace-sacen mutane, inda makonni biyu da suka gabata wasu mahara suka farma wani rukunin gidajen ma’aikatan Hukumar Filaye Jiragen Sama ta Kasa da ke Kaduna tare da yin awon gaba mutane 11 wanda kawo yanzu ba a san inda suke ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Gwamnatin Najeriya Ta Shirya Da ASUU

 An kai matsaya tsakanin Kungiyar Malaman Jami'o'i ASUU in da gwamnatin tarayya ta amince da bukatunsu. A jiya jumu'a dai ne suka yi wani zama don ganin malaman sun janye yajin aikin da ya dauki watanni bakwai ana yi. A yanzu dai gwamntin Najeriya ta amince da cire malaman daga tsarin albashi na IPPIS wanda suka jima suna turjiya akai, kuma za ta biya malaman albashin duk watannin da su ke bi. Haka ma ministan kwadagon Najeriya Cris Ngige ya tabbatarwa manema labarai cewa, za a karawa malaman jami'ar alwus da zai kai naira biliyan 35 sabanin yadda yake a da na biliyan 30. Ngige ya kuma ce za a ci gaba da tattaunawa kan sabon tsarin albashi na UTAS muddin an kammala tsara shi. A nasu bangare kungiyar malaman jami'o'in sun yi maraba da wannan yunkuri, in da ake ganin matakin ga alama zai iya kawo karshen dogon yajin aikin da aka dade ana yi.

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra. Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa. Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta. Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya. Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin. Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba? GA AMSA:  Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da saura...