Skip to main content

"Ba Zan Taba Sulhu Da 'Yan Ta'adda Ba" - In ji El-Rufa'i

Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Tufa'i ya ce ba zai taba yin sulhu da 'yan bindigar da suka sace dalibai 39 a jihar Kaduna ba.
Ya ce, "ta yaya za ka dauki kudi ka ba dan ta'addan da zai yi amfani da shi ya sayi makamai wanda zai yi amfani da shi a kan ka".

A makon da ya gabata, ‘yan ta’adda sun sace dalibai 39 tare da neman kudin fansa har Naira miliyan 500 daga Gwamnatin Kaduna.
Gwamnan ya fada a watan jiya cewa ba zai taba yin sulhu da duk wani dan fashi da makami don neman kudin fansa ba.
Jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya na fuskantar yawan sace-sacen mutane, inda makonni biyu da suka gabata wasu mahara suka farma wani rukunin gidajen ma’aikatan Hukumar Filaye Jiragen Sama ta Kasa da ke Kaduna tare da yin awon gaba mutane 11 wanda kawo yanzu ba a san inda suke ba.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey