Skip to main content

Duk Layin Kiran Da Ba A Hada Da Lambar Katin Dan Kasa Ba Za A Rufe Shi - Pantami

Ministan Sadarwar Najeriya Dakta Isah Ali Pantami ya nanata matsayarsa na tabbatar da an dakatar da sayar da layukan kira tare da tsayar da yi wa sabbin layukkan rajista.

Ya bayyana hakan a lokacin taron da ya gudanar da masu ruwa da tsaki a bangaren sadarwa, da suka hada da Hukumar Da Ke Sanya Ido Kan Harkokin Sadarwa NCC da Hukumar Bunkasa Fasahar Zamani Ta Kasa NITDA da Hukumar Samar Da Katin Shaidar Zama Dan Kasa NIMC da sauran kamfunnan sadarwar wayoyin hannu na  MTN, Glo, Airtel, Etisalat ko 9mobile da sauran su.
A wajen taron ministan sadarwar ya umurci kamfunnan su kiyaye dokoki da sharuddan da aka gindaya, kazalika dukan kamfunnan sadarwar wayoyin hannu su tilasta duk mai amfani da layukansu da ya hada layinsa na kira da lambar katinsa na shaidar zama dan kasa domin tabbatar da shi.
Sun kuma tattauna akan cewa za a soma wannan daga yau din nan laraba 16 ga Disamban 2020 zuwa ranar laraba 30 ga wannan watan na Disamban 2020, wanda daga nan za a rufe layin duk wanda bai bi umurnin ba.
Wannan matakin da aka dauka na da alaka da kokarin magance matsalar tsaro da ke ci gaba da kamari a Najeriya.

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Turai na fuskantar tsananin zafi

Burtaniya  Wani matsanancin yanayin zafi ya karaɗe yammaci da arewacin Turai, inda yanayin zafi ya zarta yadda aka saba sosai, kuma ya kai yanayin da aka jima ba a gani irinsa ba a ƙasasahe da dama. Birtaniya da Faransa sun fuskanci yanayin zafin da ba su taɓa ganin irinsa ba a watan Mayu, yayin da iska mai huci ta sa zafin ya kai ƙoluwar da ba a saba ganin irinsa ba ko da a lokacin tsanananin zafi.  Paris a Faransa  Jami’an kula da yanayi sun yi gargaɗin cewa yanayin zafin wata alama ce ta ɗumamar duniya.