Skip to main content

Jahohin Zamfara, Kaduna Da Jigawa Sun Bada Umurnin Rufe Makarantun Boko

Jahar Jigawa ta bayar da umurnin rufe makarantun Boko daga yau din nan laraba har zuwa wani lokacin da ba a bayyana ba.
Jahohi irin su Kaduna, Kano da Sokoto sun bi sahu. Wannan mataki dai a cewar gwamnatin jahar jigawa na da alaka ne da matsalar ci gaba da yaduwar annobar korona. Amma da dama na ganin hakan bai rasa nasaba da harin da 'yan bindiga suka kai a wata makarantar kimiyya ta kwana da ke Kankarar jahar Katsina ranar jumu'ar da ta gabata ne, in da ake jin sun yi awon gaba da dalibai kusan 500.
A jiya kungiyar Boko Haram ta fito ta yi ikirarin daukar alhakin sace yaran, abinda ya jefa tsoro da zullumi a zukatan al'umma.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...