Skip to main content

Da Dumi Dumi - An Bude Iyakokin Najeriya Hudu

Gwamnatin Najeriya ta bayar da umurnin bude kan iyakokita a yau din nan, da suka hada da ta Sokoto a garin Illela da Seme daga kudu maso yamma da Mfun ta kudu maso kudu da kuma ta Maigatari a jahar Katsina.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya bayar da wannan umurnin ta hannun mai ba shi shawara kan shafukan sada zumunta Bashir Ahmad, wanda ya wallafa a shafinsa na tweeter.
An dai kwashe fiye da shekara daya iyakokin na kulle, a bisa dalilan tsaro da hana fasa kwabrin shinkafa da miyagun kwayoyi zuwa cikin kasar.
'Yan Najeriya da dama ne suka shiga halin matsi sakamakon rufe kan iyakokin, in da tsada da karancin kayan masaruhi suka kai wani mataki da ba a saba ganin irin sa ba a Najeriya.
Da dama daga kasashe makwabta da suka hada da Gana da Jamhuriyar Nijar da Kamaru, sun sha matsin lamba da a bude iyakokin domin samun damar huldar cinikayya tsakaninsu da Najeriya. Hasalima ana ganin wannan na daya daga dakilan da suka haifar da rashin jituwa tsakanin Najeriya da kasar Gana, da ta kai ga gwamnatin kasar sallamo da dama daga 'yan kasar kafin daga bisani a kai ga sasantawa.
To amma kuma, galibin jama'a na mamakin bayar da wannan umurni kwatsam, a daidai lokacin da kasar ke cikin halin tsaka mai wuya dangane da tsaro, wanda kwanan nan ma wasu mahara suka sace yara 'yan makaranta kimanin 500 a jahar Katsina, da kuma ake fargabar suna iya amfani da wanna dama don tsallakawa da yaran zuwa makwabtan kasashe.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...