Skip to main content

Da Dumi Dumi - An Bude Iyakokin Najeriya Hudu

Gwamnatin Najeriya ta bayar da umurnin bude kan iyakokita a yau din nan, da suka hada da ta Sokoto a garin Illela da Seme daga kudu maso yamma da Mfun ta kudu maso kudu da kuma ta Maigatari a jahar Katsina.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya bayar da wannan umurnin ta hannun mai ba shi shawara kan shafukan sada zumunta Bashir Ahmad, wanda ya wallafa a shafinsa na tweeter.
An dai kwashe fiye da shekara daya iyakokin na kulle, a bisa dalilan tsaro da hana fasa kwabrin shinkafa da miyagun kwayoyi zuwa cikin kasar.
'Yan Najeriya da dama ne suka shiga halin matsi sakamakon rufe kan iyakokin, in da tsada da karancin kayan masaruhi suka kai wani mataki da ba a saba ganin irin sa ba a Najeriya.
Da dama daga kasashe makwabta da suka hada da Gana da Jamhuriyar Nijar da Kamaru, sun sha matsin lamba da a bude iyakokin domin samun damar huldar cinikayya tsakaninsu da Najeriya. Hasalima ana ganin wannan na daya daga dakilan da suka haifar da rashin jituwa tsakanin Najeriya da kasar Gana, da ta kai ga gwamnatin kasar sallamo da dama daga 'yan kasar kafin daga bisani a kai ga sasantawa.
To amma kuma, galibin jama'a na mamakin bayar da wannan umurni kwatsam, a daidai lokacin da kasar ke cikin halin tsaka mai wuya dangane da tsaro, wanda kwanan nan ma wasu mahara suka sace yara 'yan makaranta kimanin 500 a jahar Katsina, da kuma ake fargabar suna iya amfani da wanna dama don tsallakawa da yaran zuwa makwabtan kasashe.

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Murtala Abdulkadir Dan Iya Gambun Sakkwatawa

Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya ya shahara wajen ayyukan jinƙai a Jihar Sokoto tsawon  shekarun ya zuwa yanzu. Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto  A tattaunawar da jaridar Tantabara News ta yi da Nura Muhammad Chiso, wanda ke jagorancin daya daga cikin ƙungiyoyin Alhaji Murtala Abdulkadir Dan Iya, mai suna da ke bayar da tallafi da wayar da kan al'umma a jihar ta Sokoto, ya bayyana tarin manyan tallafan da wannan shahararren ɗan kasuwa, kuma ɗan siyasa ya yi wa dubban mutane mabukata a jihar, lamarin da ya ƙara ɗaukaka darajar sunansa a cikin jihar da ma wajenta. N ura Muhammad Chiso  Nura Muhammad Chiso ya ce, "wannan aikin alheri na shugaban Hukumar Bayar Da Tallafin Ƙaro Karatu ta Jihar Sokoto, wani babban aikin alheri ne da ya gane dubban jama'a talakawa har hakan ya sa suke kiran sa da gambun Sakkwatawa saboda faranta musu rai da yake yi". Ga wa...