Skip to main content

'Yan Bindigar Da Suka Sace Dalibai A Jahar Katsina Sun Ce Kada Su Sake Jin Shawagin Jirgin Sama Kusa Da Su

A jiya ne daya daga iyayen yaran da mayakan suka dauke ya sanar da hukumomi cewa 'yan bidigar sun kira shi ta waya, in da suka yi gargadin cewa a tabbatar wani jirgin saman yaki bai sake ci gaba da shawagi a kusa da in da su ke ba, idan ba haka ba za su dauki matakin da ya yi mu su daidai.
Rahotanni da ke fitowa yanzu haka na cewa maharan sun tafiyar da ta kai dazukan jahar Zamfara da yaran, kuma sun fara tattaunawa don neman kudin fansa kafin su kai ga sakin su.
A yau gwamnan jahar Katsina Aminu Bello Masari, ya sanar da manema labarai cewa, an kai ga gano yara 17 daga cikin wadanda suka tarwatse a daji, ina da tun jiya aka sada su da iyayensu.
A ranar jumu'a da ta gabata dai ne wasu 'yan bindiga da ba a kai ga ganowa ba suka yi awon gaba da yaran, koda ya ke jiya litinin shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau, ya bayyana cewa su suka sace yaran.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey