Skip to main content

Kwalejin Ilmi Ta Sokoto Za Ta Koma Jami'ar Ilmi Ta Sokoto - Tambuwal

Gwanan jahar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya lashi takobin ganin kwalejin Ilmi ta Shehu Shagari ta koma Jami'ar Horas da Malamai da Fannonin Ilmi Ta Jahar Sokoto.
Ya fadi hakan yau litinin a lokacin bukin cikar kwalejin shekaru 50 da kafuwa, karo na 22.
Ya yi karin hasken cewa ganin yadda ya dauki sha'anin ilmi da muhimmanci da ma yadda ya ke ware masa kaso mafi tsoka a kasafin kudin gwamnatinsa, zai gana da masu ruwa da tsaki a fannin ilmi da ma mai alfarma Sarkin musulmi don neman shawara akan wannan batu.
Ya kara da cewa zai kara ginawa kwalejin karin dakunan kwanan dalibai, domin saukake matsalar cin koso.
To amma kuma, wasu da TANTABARA ta zanta da su, na kallon batun a matsayin irin alkawurran  da ya ta bayi na samar da karin Sassan nazarin ilmin kimiyya da liktanci a Jami'ar Jahar Sokoto,  tun shekaru uku da suka gabata, amma suka zama durmukyal da suka ce kalamai ne na rufa ido kawai da ya saba da su.
To, sai dai aikin gina asibitin koyarwar jami'ar da ke ci gaba da yi yanzu haka, na nuna alamun share hanya ga alkawarin da gwamnatin jahar ta Sokoto ta dauka a wancan lokaci.
Yanzu dai lokaci ne zai tabbatar da wannan batu sabo.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Wata Mota Cike Da Harsasan Bindiga Ta Fada Rami A Garin Awka Na Jahar Imo

Hankalin jama'a yayi matukar tashi a jiya Lahadi biyo bayan gano wata babbar mota cike da harsasai masu rai a birnin Anacha na jahar Imo da ke kudu maso gabashin tarayyar Najeriya. Rahotannin da suka shigo muna na cewa jami'an tsaron cikin hanzari sun afkawa garin na kasuwanci domin daukar matakin gaggawa kan lamarin.  Babbar motar wadda ke dauke da kwaliyoyin harsasai masu rai ta fada cikin wani rami da ke kan titi, inda dukan harsasan suka zube. Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce: “Motar ta fadi, kuma duk titin na cike da harsasai.  Wasu yaran ma sun debi wasu da hannayensu suka gudu, kafin jami’an tsaro su iso wurin. ”  Majiyar ta ci gaba da bayyana cewa direban babbar motar da mai yi masa hidima sun yi watsi da motar bayan hatsarin ya faru, inda suka yi batan dabo zuwa inda ba a sani ba. Amma wata majiyar ta ce ‘yan sanda sun cafke direban. “Lamarin ya jawo jami'an tsaro masu yawa zuwa yankin hanyar Awka da da safiyar yau. 'Yan sanda sun...

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

An Ruguza Makarantar Malam Abduljabbar Kano

Dazu dazun nan gwamnatin jahar Kanon ta tura jami'an ma'aikatar lura da tsarin filaye in da ta ruguza makarantar Malam Abduljabbar. Gwamnatin dai ta taba bayyana cewa filin da ya ke amfani da shi haramtacce ne, in da ta kai ga kwace shi tare da bada umurnin gudanar da wasu muhimman ayukka a wurin. Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin gwamnatin jahar Kano da Abduljabbar in da a ranar laraba sakataren watsa labaran gwamnatin jahar, Muhammad Garba ya bayar da sanarwar rufe masallacin Malam Abduljabbar tare da hana masa gudanar da wa'azi baki daya. In da ta ce hakan na da alaka da irin yadda ya ke tunzura jama'a a kalaman da ya ke amfani da su a lokacin da ya ke da'awa.

Gunmen Abducted 11 FAAN Staff In Kaduna

A group of gunmen yesterday attacked the residences of the Federal Airport Authority of Nigeria Kaduna. Reports say gunmen stormed the compound and abducted at least 11 people. Recent reports suggest that the bandits also abducted a staff of  Nigerian Airspace Management Agency NAMA, his wife, a National Meteorological Agency (NIMET) official and his children.Their whereabouts are still unknown. Kidnappings are common in Nigeria today, and almost every morning there are reports of killings or kidnappings for ransom. Last week Nigerian President Muhammadu Buhari vowed to end abduction in Nigeria but for all indications his words were not effective.

Breaking: Chadian President Idris Deby Is Dead

  Chadian President Idris Deby died while leading the country's security forces over the weekend, fighting rebels on the northern country's border with Libya.  President Deby is widely expected to win the country's general election by 80 percent after seeking a sixth term.  The military has dissolved parliament and announced that it would hold power for 18 months before new elections.  Idris Deby took power in Chad in 1990 after overthrowing the government of former President Hissene Habry, and has ruled Chad for 30 years.

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."

Dalar Amurka Na Fuskantar Barazanar Durkushewa

Shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya soki kasar Amurka akan irin rawar da dala ke takawa a tattalin arzikin duniya tare da yin kakkausar suka ga asusun lamuni na duniya na IMF. Lula ya yi waɗannan kalamai a wata ziyarar aiki da ya kai Chana, jiya Alhamis a birnin Shanghai a wani bikin kaddamar da takwaransa, Dilma Rousseff a matsayin sabuwar shugabar bankin raya kasashen BRICS, da gamayyar kasashenn Brazil da Rasha da Indiya da Chana da kuma Afirka ta Kudu suka samar. "Me ya sa kowace ƙasa za a danganta da dala don kasuwanci? Wanene ya yanke shawarar dala za ta zama kuɗin duniya?"  Ya ƙara da cewa me yasa banki kamar bankin BRICS ba zai iya samun kuɗin da zai gudanar da hulɗar kasuwanci tsakanin Brazil da Chana ba, da ma sauran ƙasashen duniya? Ya ce yana mamakin yadda ƙasashe cike da rauni  su ke bin sawun amfani da dala wajen gudanar da kasuwanci alhali suna iya hakan da kuɗaɗensu. A wata ganawa tsakanin sa da shugaban Chana Xi Jinping, da kuma ya ...

Nigerian President Vaccinated Against Covid-19

Nigerian President Muhammadu Buhari and his vice president, Professor Yemi Osinbajo, have been vaccinated with AstraZeneca vaccine, just one day after the nationwide vaccination campaign. Earlier, the Federal Government announced that as soon as the vaccine arrives in Nigeria, the President, government officials and all Governors will be at the forefront of the immunization drive which would be shown on the National Television (NTA) to set an example for other Nigerians, as well as allay their fears about the legitimacy of the vaccine. The president's doctor, Dr. Shuaibu Rafindadi, vaccinated the president at 11:53 a.m. Nigerian time (10:53 a.m. GMT) on Saturday, and Vice President Yemi Osinbajo immediately joined the process. They were also provided with electronic immunization cards by the Director General of Primary Health Care Development (NPHCDA), Dr. Faisal Shuaib. Nigeria successfully started the vaccination on Tuesday, becoming the third West African country to ...

Kungiyar Boko Haram Ta Saki Bidiyon Yaran Da Aka Sace A Katsina

Kungiyar Boko Haram ta saki wani faifan bidiyo da ke nuna yaran nan daliban makarantar kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina, kwanaki biyar da sace su. A cikin bidiyon an ga wani yaro mai kimanin shekaru sha biyar na magana cikin Hausa: "Don Allah ina rokon gwamnati da kada ta yi amfani da duk wasu 'yan sa kai, a rufe dukan makarantu. Kuma sojojin da ke tafe don taimakonmu don Allah su koma, ba za su iya yi wa (mayakan) kome ba". In ji yaron. A can bayan yaron an ga wasu yara kanana masu yawan gaske da ake umurta da su zauna, kuma da ba su fi shekara goma goma ba, suna kuka tare da rokon a taimaka a cece su daga hannun mayakan. Faifan bidiyon mai tsawon minti daya ya nuna yaran cikin kura da alamar gajiya a tattare da su, sakamakon tafiya mai nisa a kasa. Ana kuma jin muryar daya daga 'yan bindigar na gargadin gwamnati da kada ta dauki kowane matakin amfani da karfi. Yana mai jaddada cewa yaran na cikin koshin lafiya. A ranar jumu'ar da ta gabata ne maharan suka y...