Skip to main content

Kwalejin Ilmi Ta Sokoto Za Ta Koma Jami'ar Ilmi Ta Sokoto - Tambuwal

Gwanan jahar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya lashi takobin ganin kwalejin Ilmi ta Shehu Shagari ta koma Jami'ar Horas da Malamai da Fannonin Ilmi Ta Jahar Sokoto.
Ya fadi hakan yau litinin a lokacin bukin cikar kwalejin shekaru 50 da kafuwa, karo na 22.
Ya yi karin hasken cewa ganin yadda ya dauki sha'anin ilmi da muhimmanci da ma yadda ya ke ware masa kaso mafi tsoka a kasafin kudin gwamnatinsa, zai gana da masu ruwa da tsaki a fannin ilmi da ma mai alfarma Sarkin musulmi don neman shawara akan wannan batu.
Ya kara da cewa zai kara ginawa kwalejin karin dakunan kwanan dalibai, domin saukake matsalar cin koso.
To amma kuma, wasu da TANTABARA ta zanta da su, na kallon batun a matsayin irin alkawurran  da ya ta bayi na samar da karin Sassan nazarin ilmin kimiyya da liktanci a Jami'ar Jahar Sokoto,  tun shekaru uku da suka gabata, amma suka zama durmukyal da suka ce kalamai ne na rufa ido kawai da ya saba da su.
To, sai dai aikin gina asibitin koyarwar jami'ar da ke ci gaba da yi yanzu haka, na nuna alamun share hanya ga alkawarin da gwamnatin jahar ta Sokoto ta dauka a wancan lokaci.
Yanzu dai lokaci ne zai tabbatar da wannan batu sabo.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...