Skip to main content

Gwamnatin Nijeriya Ta Karyata Kashe Masu Zanga-Zanga A Lekki

 Minjstan watsa kabaran Najeriya Alhaji Lai Muhammad ya karyata rahoton kafar yada labaran CNN da ke cewa sojoji sun harbi da dama daga masu zanga-zangar Endsars a Lekki ta jahar Legas.

Ministan ya shaidawa manema labarai hakan inda ya ce gwamnatin Najeriya za ta dauki mataki kan batun, da ya hada da rubutawa kafar ta CNN wasika akan ta karyata rahoton ko kuma duk abinda ya biyo baya kada su yi nadamarsa.

A cikin wani bidiyo da kafar ta watsa an nuna sojoji na harbin masu zanga-zangar da harsashe na kwarai; har ma an ga wasun da aka harba kwance cikin jini.

To sai dai tun a watan Oktoban da lamarin ya faru, hukumomin kare hakkin dan Adam da suka hada da Amnesty International suka fitar da rahotannin zargin harbin bindigar da ake alakantawa da jami'an soji.



Comments

Wadanda aka fi karantawa

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...