Skip to main content

'Yan Majalisa Sun Nemi Buhari Ya Yi Garambawul Ga Manyan Jami'an Sojoji

'Yan majalisar dattawan Najeriya sun bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake lale akan sha'anin tsaro. 'Yan majalisar dai sun nemi Buhari ya yiwa manyan hafsoshin sojin kasar garambawul, tare da sanya sabbin jini. 
Sanata Kashim Shatima ya bayyana damuwarsa tare da shawartar shugaban kasa da ya sa a yi bincike kan lamarin tare da tabbatar da an magance matsalar tsaro a yankin arewa maso gabas. Shatima ya ce "wannan lamari ne da ya zama wajibi a dauki tsattsauran mataki game da shi".
Shi ma sanata Adamu Aleiro daga jahar Kabi, a wani sako da ya aike a rubuce, ya bayyana cewa, "bai kamata shugaba Buhari ya aike da tawaga a jahar Borno don yin jaje ba, da kan sa ya dace ya je".
Aleiro ya kuma shawarci shugaba Buhari da yayi garambawul ga manyan jami'an sojoji Najeriya tare da maye su da sabbin jini.
Rikicin Boko Haram dai ya kwashe shekaru 11 yana addabar yankin arewa maso gabascin Najeriya, kuma yayi sanadiyyar hallakar dubban rayuka gami da hasarar dukiya.
A 'yan shekarun nan dai matsalar tsaro ta addabi yankunan arewacin Najeriya, wanda baya ga ayukan 'yan ta'adan Boko Haram da kungiyar mayan IS, shiyar arewa maso yamma na fuskantar matsalar 'yan bindiga masu garkuwa da mutane don neman kudin fansa, a jahohin Zamafara da Sokoto da Katsina da sauran su.
Idan ana iya tunawa dai, ranar jumu'ar da ta gabata ne mayakan kungiyar Boko Haram suka kashe a kalla manoman shinkafa 43 a kauyen Zabarmari na jahar Borno.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey