Skip to main content

Gwamnatin Tambuwal Na Shirin Ba Da Mamaki

Gwamnatin jahar Sokoto ta yunkoro wajen samar da ayukkan raya gari, tun daga soma aikin Asibitin Koyarwa ta Jami'ar Jahar Sokoto da kuma Makarantar 'Yan Mata da ke garin Kasarawa galibin mazauna jahar ke ganin cewa an soma samun sauyi.
Ganin yadda aka soma wasu ayukan da aka yi shekaru ana jira. Kuma cikin sauri da kamala.
Tun lokacin zuwan gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal a 2015, galibin jama'a ke fadin albarkacin baki ganin gudanar da ayukkan kamar da wasa. To sai dai kuma, gwamnatin ta bayar da kwangiloli da suka hada da gina gadojin sama guda biyu da aka ce za a gina nan take. Kazalika da samar da filin wasa katafare da aka ambata da sauran su.
TANTABARA ta zanta da wasu mazauna yankunan da ake ayukan in da suka shaida mata cewa suna murna da samar da ci gaban idan har ya tabbata. Haka ma wasu da dama sun soma samun hanyar abin kaiwa bakin salati daga soma ayukkan, inda suka kakkafa sana'o'insu a wuraren.
A ziyarar da TANTABARA ta kai wuraren ta lura cewa a yadda aikin ginin makarantar da sibitin ke tafiya akwai yuwar kammala su a daidai lokacin da aka shata. 
To sai dai, don tabbatar da hakan, ta yi kokarin hira da babban injiniyan da ke lura da aikin, injiniya Abu Salma amma ya ki amincewa, wakilinmu ya kira wayarsa tare da tura masa sakon kar-ta-kwana amma kawo wannan lokaci bai amsa ba.
Wasu ra'ayoyin mazauna jahar kuma na cewa, sai gwamnatin Tambuwal ta yi da gaske domin ganin ta sha gaban gwamnatocin da suka gabace ta dangane da ayukan raya jaha. To amma kuma a cewar magoya bayan gwamnatin hakan bai rasa nasaba da karyar tattalin arzikin Najeriya sabanin a can baya, wanda ba gwamnatin Tambuwal ce kadai ta fuskanci hakan ba..

Comments

Popular posts from this blog

Iran seeks talks with us after threat of attack – Trump

U.S. President Donald Trump has said that Iranian authorities have contacted the United States to seek talks, following his threat to take military action over the killing of protesters in the country. Trump made the statement while speaking to journalists, saying that a meeting between the two sides has already been planned, but that the United States might take some action before the meeting takes place. Meanwhile, a human rights organization in Iran says it has confirmed the deaths of nearly 500 people since the outbreak of the protests. Likewise, some circulating video clips show a site outside Iran where bodies are being kept, with people going there to search for the remains of their relatives who have gone missing.

WHEN LIES GO VIRAL: DEFENDING TRUTH IN NIGERIA AND WEST AFRICA’S DIGITAL PUBLIC SPHERES

Across Nigeria and West Africa, digital technology has reshaped how citizens engage with information, governance, and public debate. Mobile phones and social media platforms have become dominant sources of news, especially for young people and communities with limited access to traditional media. While this transformation has expanded civic participation and freedom of expression, it has also intensified the spread of misinformation, posing serious risks to democracy, public health, and social cohesion. Misinformation is no longer a marginal problem. It is a structural challenge that affects elections, security, development communication, and trust in public institutions. Addressing it requires coordinated action that combines ethical journalism, media literacy, platform accountability, and evidence based policy responses. THE DIGITAL INFORMATION LANDSCAPE IN NIGERIA AND WEST AFRICA Nigeria is Africa’s most populous country and one of its most digitally active societies. So...

Turai na fuskantar tsananin zafi

Burtaniya  Wani matsanancin yanayin zafi ya karaɗe yammaci da arewacin Turai, inda yanayin zafi ya zarta yadda aka saba sosai, kuma ya kai yanayin da aka jima ba a gani irinsa ba a ƙasasahe da dama. Birtaniya da Faransa sun fuskanci yanayin zafin da ba su taɓa ganin irinsa ba a watan Mayu, yayin da iska mai huci ta sa zafin ya kai ƙoluwar da ba a saba ganin irinsa ba ko da a lokacin tsanananin zafi.  Paris a Faransa  Jami’an kula da yanayi sun yi gargaɗin cewa yanayin zafin wata alama ce ta ɗumamar duniya.