Skip to main content

AN KUSA SHAWO KAN CUTAR COVID-19

 Rahotanni da ke fitowa yanzu haka sun bayyana cewa sabbin magungunnan rikagakafin cutar korona na nuna alamaun tasiri cikin gaggawa. 

Kamfunnan Pfizer da BioNtech ne sahun gaba wajen samar da maganin, wanda an yi gwajinsa akan kimanin mutum 43,000 a kasashen duniya daban-daban tare da lura da cewa yana kashe cutar da kashi 94.5 kuma ba hi da illa.

Masana kiyon lafiya a duniya dai sun bayar da shawarar ci gaba da amfani da rigakafin, sakamakon amanna da suka yi da shi.

Ana sa ran samar da adadi mai yawa da zai wadaci al'ummar duniya nan da karshen shekara mai kamawa ta 2021, wanda ake muradin samun kimanin biliyan daya da doriya.

Annobar korona da ta bulla tun a farkon 2020 ta kawowa duniya koma baya, wanda galibin kasashe masu karfin tattalin arziki suka gamu da cikas a bangaren tattalin arzikin, wanda ya shafi sassa da dama da suka hada da suhuri da yawo bude ido da ma cinikayya.

Wannan yunkurin samar da rigakafin dai ana daukar sa a matsayin sabon kandagarki ga annibar Covid-19.


Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey