Skip to main content

Da Dumi Dumi - Daliban Makarantar Kimiyya Ta Kankara Sun Iso Gida

Yanzu yanzun nan daliban da aka sace a Makarantar Kimiyya da Fasaha ta Kankara da ke jahar Katsina suka iso gida.
Yaran su kimanin 340 cikin rakiyar jami'an tsaron soji da 'yan sanda, sun iso fuskokinsu cike da annuri, koda yake dukan su sun yi butu-butu da kura alamar wahala.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi waya da gwamnan jahar Katsina Aminu Bello Masari in da ya taya shi murnar samun nasarar ceto yaran.
An dai sace yaran a ranar jumu'a da dare da ta gabata a wata makarantar kwana da ke karamar hukumar Kankara a jahar ta Katsina.
Gwamnatin jahar ba ta yi cikakken bayanin yadda aka karbo yaran ba, ko da ya ke a bidiyon da kungiyar Boko Haram ta fitar da rana an ji wani mai garkuwa da yaran na fadin suna tattaunawa da gwamnati don karbar kudin fansa.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey