Skip to main content

Ba Zamu Bar Korona Ta Haifar Muna Da Bashin Da Zai Ruguza Mu Ba - Antonio Gutarres

 A yau jumu'a sakataren Majalisar Dunkin Duniya, Antonio Gutarres ya bayyana cewa dimbin bashin da annobar korona ta jefa duniya ya wuce misali, baya ga yunwa da tashin hankali da sauran matsaloli da ke addabar kasashe musamman masu tasowa.

Yana wadannan kalamai ne daidai lokacin da a karshen makon nan ake shirin gudanar da taron kolin kasashe ashirin masu karfin tattalin arziki na duniya da aka fi sani da G-20. 

Ya ce bai kamata bashi ya zama tarnaki ga ci gaban duniya ba. Ana ganin yana wannan magana ne da manufar tursasa manyan kasashe masu arziki da su yi sassauci ga matalautan kasashe a bangaren da ya shafi dimbin bashin da ake bin su.

Gutarres ya ce, "kasashe masu arziki kamar Amurka da China ya dace su samar da sassauci da daidaito ga kasashe masu tasowa, domin taimaka mu su farfadowa".

Ya yi nuni da irin illar da kin hakan za ta iya haifarwa duniya nan gaba, "kusan hanyar samar da kandagarkin Covid-19 ba ta wuce ta kudi ba, kenan bai dace a ce duk rana ta Allah muna dora bashin biliyoyin kudaden a wuyan al'umma mai tasowa ba", in ji Gutarres.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Wanene Ɗan Jarida?

Ɗan jarida mutum ne kamar kowa, sai dai tunaninsa da manufofinsa kan tafi daidai ne kawai da ra'ayin MASU SAURARO ta fuskokin da suka shafi aikinsa. Ya zama mai wakiltar waɗanda ba su da baki ne ko kafafuwan zuwa, kuma idanuwan talakawa a kowane lokaci. Idan ka nuna ma sa launi shuɗi, ƙoƙarin ya ke ya tabbatar da launin nan shuɗi ne ziryan ko yana da garwaye? Idan ka ce ma sa labarin abu kaza ya faru, ba zai ce a'a ba kuma ba zai ce eh ba, aikinsa shi ne TABBATARWA . Idan mai sauraro namiji ne ko mace ko mai ra'ayin wani addini ko akida ko mai kuɗi ko talaka, ɗan jarida kan GIRMAMA kowa, kuma zai ɗauki kowa a matsayin DAIDAI ta fuskar ba su damar bayyana ra'ayoyinsu. Ɗan jarida kan tafi da zamani, ya kuma rungumi fasahar da ƘIRƘIRA ta kawo domin tafiya daidai lokaci. A kowace marra GASKIYA ita ce madogarar ɗan jarida, kuma wannan kan ƙara sa masu sauraro su amince da shi. Amma kuma, dole ne ɗan jarida ya zama MAI IKON KANSA , ba zai yi ma kowa alfarma b...

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...