Skip to main content

Mai Tsaron Lafiyar Kakakin Majalisar Wakilai Ta kasa Ya Harbe Mai Sayar Da Jarida

 A jiya da yammaci ne dai lamarin ya faru in da daya daga jami'an da ke kare lafiyar kakakin majalisar wakilai na kasa, Femi Gbajabiamila ya yayi harbin da yayi sanadiyyar mutuwar wani mai tallar jarida.

Gbajabiamila ya wallafa a shafinsa na tweeter cewa, yana kan hanyar dawowa ya tsaya wajen don gaisawa da mutane, to sai wasu gungun mutane suka taso masa abinda ya sa masu tsaron lafiyarsa suka yi harbi, wanda ta kai ga samun daya daga cikin masu sayar da jaridun da ke wurin.

Bayanan da TANTABARA ta samu na cewa an dakatar da jami'n da ake zargi da yin harbin, har sai an kammala bincike.

Galibin lokuta ana zargin jami'an tsaron Najeriya da yin harbin da kan jawo hallakar mutane, wanda ko kwanan baya irin haka ta faru a Kano in da ake zargin jami'an tsaron 'yan sanda da hallaka wasu mutane uku bisa harbin da ake zargin na kuskure ne.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey