Skip to main content

Barayi Sun Yiwa Ofishin Jaridar Daily Star Nigeria Kaf

A yau da rana wasu gungun barayi da ba a kai ga ganowa ba sun kai samame ofishin jaridar Daily Star Nigeria da ke jahar Sokoto.

Babban editan jaridar, Dr. Mansur Isah Buhari ya tabbatar da wannan lamari, in da ya ce barayin sun yi awon gaba da wasu muhimman kaya da suka hada da kananan kwamfutoci, da akwatin talabijin da ma wasu kudaden da ba a bayyana adadinsu ba kawo yanzu.
Dr. Mansur ya ce, "kamar yadda al'adar ofishinmu ta ke, wakilanmu na wajen nemo labarai ni kai na ma na dan fita bana wajen, lokacin da barayin suka auni hakan tare da fasa kofar ofishin in da suka wawushe kome".
Jaridar Daily Star Nigeria dai na cikin na gaba gaba daga cikin jerin jaridun yanar gizo da ake da su a Nijeriya yanzu haka.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey