Skip to main content

Rikicin Jam'iyyar PDP A Kudu Maso Yamma

 

 Rikicin jam’iyar PDP a yankin kudu maso yammacin Najeriya na cikin kwale-kwale tun bayan da aka zabi gwamnan jahar Oyo Seyi Makinde jam’iyar PDP ke ganin ya na uwa da makarbiya a dukan lamurran da suka shafi jam’iyar, abinda suka ce na neman mayar da hannun agogo baya; kuma lamarin da wasu shuwagabannin jam’iyyar ke ganin shisshigi ne da kuma tare hanyar wasu.

A baya bayan nan gwamna Makinde ya dinga kai kawo a rikicin jam’iyar a jahar Ikiti da ya ce neman sulhu ne da shiga tsakani, amma hakan ya kai ga musayar yawu tsakaninsa da gwamnan jahar Peter Fayose na lokacin, wanda ke yiwa gwamnan jahar Oyon kallon mai goyon bayan Sanata Abiodun Olujinmi da ya tsaya takara tare da shi.

A halin yanzu an ji gwamnan na jahar Oyo na kurari da nuna goyon baya akan shari'ar da ake yi wa Fayose, in da Makinde ke ganin ya dace Hukumar Yaki da Zarmiyar Dukiyar Al’umma ta EFCC ta ci gaba tuhumar tsohon gwamnan jahar Ikitin.

Rahotanni sun ce an jiyo shi ya na cewa, duk yadda Fayose ya yi don kare kan sa, babu shakka sai an daure shi akan lafin da ya tafka. 

Da dama dai dag jiga-jigan jam’iyar PDP  yankin na Yarbawa na ganin kalaman a matsayin barazanar wargajewar jam'iyyar.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Binani Na Neman Kotu Ta Tabbatar Da Ita Wadda Ta Lashe Zaɓen Adamawa

Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Adamawa a ranar Litinin sun fito kan tituna domin nuna adawa da ayyana Sanata Aishatu Dahiru Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa. Sai dai ita Binani ta buƙaci wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) daga sauya matakin da aka ɗauka na ayyana ta da a ka yi a matsayin wadda ta lashe zaɓen.  A wata buƙata da ta shigar a ranar Litinin, mai neman izinin kotun ya nemi izinin kotun ta ba ta damar shigar da buƙatar neman umarnin haramtawa INEC daga ɗaukar duk wani mataki na watsi da sanarwar da aka yi a ranar 16 ga Afrilu da Kwamishinan zaɓen jahar, Barista Hudu Ari ya ayyana ta a matsayin wadda ta samu ƙuri'u mafifi rinjaye kuma ta lashe zaɓen alhali ba a kammala tattara sakamakon zaɓen gaba ɗaya ba. Ta kuma nemi a ba da umarnin hana hukumar zabe ta INEC, da wakilinta nadawa ko kuma duk wanda ke wakiltarta daukar wasu matakai na bayyana wanda ya lashe zaben gwamna da ak...