Skip to main content

Sanwolu Da El-Rufai Sun Killace Kan Su Saboda Covid-19

Gwamnan jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i ya kebe kan sa saboda wani daga cikin iyalinsa da hadimansa sun kamu da cutar korona.
Gwamnan ya bayyana hakan a shafinsa na tweeter, in da ya ce a gobe lahadi zai je asibiti don auna shi a tabbatar idan har yana dauke da ita.
Shi ma gwamnan jahar Legas, Babajide Sanwolu ya bayyana killace kansa sakamakon samun wasu na kusa da shi dauke da cutar.
Sanwolu ya bayyana cewa wajibi ne ya kebe kan sa kafin a gudanar da gwaji, gudun kada idan ya na dauke da ita ya yadawa wasu makusanta.
Jahar Legas dai na sahun gaba daga jerin masu dauke da cutar a Najeriya. Duka jahohin biyu sun yi fama da dokar kulle a watannin baya lokacin da annobar ta yi kamari.
Kwanaki uku da su ka gabata an jiyo gwamnan jahar Kaduna Malam Nasiru El-Rufa'i, na barazanar kulle jahar muddin jama'a suka ci gaba da kin bin ka'idojin yaki da cutar korona da aka san da su.

Comments

Wadanda aka fi karantawa

INEC Ta Nemi A Kama Kwamishinan Da Ya Sanar Da Sakamakon Zaɓen Adamawa

Bayan kammala wani zaman tattaunawa a jiya talata da Hukumar ta INEC ta yi a Abuja dangane da dambarwar da ta faru a jahar Adamawa.  Hukumar ta fitar da sanarwar matakin da ta ɗauka a shafinta na twitter, inda ta yi kira ga Sifetan 'yan sanda na ƙasa da ya gurfanar tare da tuhumar tsohon kwamishinan zaɓen jahar Barista Hudu Yunusa Ari. Ta kuma nemi Sakataren Gwamnatin Tarayya da ya ja hankakin hukumomin da ke da alhakin naɗa kwamishinonin zaɓe domin ɗaukar matakin da ya dace. Wannan dambarwar ta soma ne tun daga ranar Lahadi lokacin da kwamishinan zaɓen ya ayyana A'ishatu Ɗahiru Binani a matsayin wadda aka zaɓa gwamnar jahar Adamawa gabanin a kammala tattara sakamakon zabe.

Da Dumi Dumi An Ceto Yaran Da Aka Sace A Katsina

Sakataren gwamnatin jahar Katsina Alhaji Mustapha Inuwa ya fitar da sanarwar cewa an samu nasarar ceto daliban nan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su daga makarantar kwanan ta Kimiyya da ke Kankara a jahar Katsina. Ya ce an ceto yaran su 340, kuma yanzu haka suna kan hanyarsu ta isowa jahar daga Tsafen jahar Zamfara. Ana sa ran gobe jumu'a za su gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kafin daga bisani a sada su da iyayensu. Sauran bayani zai zo nan gaba.

Takalman Fir'auna

Takalman Zinariya na Fir'auna Tutankhamun, na daula ta 18 wadda ya yi mulki shekaru 1,300 kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Yanzu haka waɗannan takalman na nan a Gidan Adana kayan Tarihi na Masarautar Alƙahira da ke Misira 📷 Saliadeen Sicey