Skip to main content

'Yan Bindiga Sun Sace Yarinya 'Yar Shekara 18 A Jahar Kabi

Rundunar ‘yan sanda reshen jihar Kabi ta tabbatar da sace wata yarinya‘ yar shekaru 18 (da aka sakaya sunanta) a Gangaren NEPA, Birnin Kabi, babban birnin jihar Kebbi a farkon safiyar yau Juma’a.
DSP Nafi’u Abubakar, jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda, ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Birnin Kabi.
Ya ce jami'a 'yan sanda sun yi duk mai yiwuwa don ceto yarinyar amma abin ya faskara
Abubakar ya shawarci jama'a da akoyaushe su dinga kai rahoton duk abinda ba su amince da shi ba, domin hakan zai taimaka wajen yakar ayukkan ta'addanci.
An kuma gano cewa mahaifin yarinyar da aka sace, Faruq Mohammed jami'in Hukumar Tsaro ta (NSCDC), ta Jihar Kabi ne.
Da yake magana a wata hira da manema labarai, Mohammed, ya ce ‘yan bindigar sun shigo unguwar ne kwaram
“Lokacin da suka zo gidana, na lura tare da jiro hayaniya kuma na fahimci cewa wani abu da ba daidai ba da ke shirin aukuwa.
“Ina da hanyoyi biyu a gidana: daya a gaba yayin da kuma dayar ke cikin gareji.
“Na yanke shawarar cewa ya kamata mu fita ta cikin gareji; cikin rashin sa'a, da bude kofar, sai muka hadu da daya daga cikin 'yan fashin dauke da muggan makamai a gefen motata, cikin hanzari muka nemi wata hanya sannan muka tsallaka zuwa gidan makwabta.
“Yan fashin sun kutsa cikin gida na suka fara bincike daki daki. abin takaici, ‘yata tana kwance a dakinta, lokacin da suka kwankwasa ta bude dakin sai suka dauke ta suka tafi da ita.”
Wata majiya mai tushe ta ce 'yan fashin sun kuma kai hari gidan wani Malam Sanusi Nagoru wanda ya yi jaruntakar tare da biyu daga cikin 'yan ta'addan kuma ya fi karfin su, ya kara da cewa mutumin ya nemi taimako daga wasu mutane.
Majiyar ta ce, babu wanda ya ba shi goyon baya don fatattakar 'yan bindigar, ta kara da cewa ba shi da wani zabi da ya wuce ya gudu da ransa.
“Da ya ga wasu‘ yan fashi sun zo su taimaka musu, sai mutumin ya ture ya ture wadannan ‘yan fashin, ya ranta a na kare.
Daya daga cikin matansa ta zo ta toshe kofar don ta hana barayin shiga babbar hanyar shiga.
Majiyar ta kara da cewa, ''Gani hakan ya sa suka bude wuta suka harbe ta a cinya, wacce yanzu haka ke amsar magani a Cibiyar Kiyon Lafiya Ta Tarayya (FMC) da ke Birnin Kabi." 

Comments

Wadanda aka fi karantawa

Gwamnatin Najeriya Ta Shirya Da ASUU

 An kai matsaya tsakanin Kungiyar Malaman Jami'o'i ASUU in da gwamnatin tarayya ta amince da bukatunsu. A jiya jumu'a dai ne suka yi wani zama don ganin malaman sun janye yajin aikin da ya dauki watanni bakwai ana yi. A yanzu dai gwamntin Najeriya ta amince da cire malaman daga tsarin albashi na IPPIS wanda suka jima suna turjiya akai, kuma za ta biya malaman albashin duk watannin da su ke bi. Haka ma ministan kwadagon Najeriya Cris Ngige ya tabbatarwa manema labarai cewa, za a karawa malaman jami'ar alwus da zai kai naira biliyan 35 sabanin yadda yake a da na biliyan 30. Ngige ya kuma ce za a ci gaba da tattaunawa kan sabon tsarin albashi na UTAS muddin an kammala tsara shi. A nasu bangare kungiyar malaman jami'o'in sun yi maraba da wannan yunkuri, in da ake ganin matakin ga alama zai iya kawo karshen dogon yajin aikin da aka dade ana yi.

Me Ku Ka Sani Game Da Labari Maras Daɗi (Negative Story)?

Galibin wasu mutane na ganin 'yan jarida ba su cika bayar da labarai ma su daɗi ba face waɗanda suka shafi tashin hankali da tonon silili da ƙwanƙwanto da kuma na haɗurra. Wannan fahimta kuwa na da nasaba da kasa fahimtar aikin jaridar kansa da wanda ke yin sa. Ni a ganina duk wani labari da ya shafi ayyukan muggan mutane da ya munanawa mutane na gari shi zan mayarwa hankali domin fallasa mai mugunta da farantawa wanda aka zalunta. Bari mu soma da mai sauƙi kafin mu duba ma su sarkakiya. Idan haɗari ya faru, misali na mota ko jirgin sama ko na kasa ko kuma gobara ko ambaliyar ruwa; za mu bayar da labarin. Shin ka san ba muna bayar da labarin ne saboda kawai a ji an mutu ko an kaririye ko an yi hasarar dukiya ba? GA AMSA:  Game da haɗari ko gobara da sauran iftila'i mu kan bayar da wannan labari saboda bayyana halin waɗanda matsalar ta rutsa da su, domin samun agajin hukumomi da masu iya tallafawa. Mu kan bayar da labarin saboda jawo hankalin hukumomin tsaro da saura...