Skip to main content

'Yan Bindiga Sun Sace Yarinya 'Yar Shekara 18 A Jahar Kabi

Rundunar ‘yan sanda reshen jihar Kabi ta tabbatar da sace wata yarinya‘ yar shekaru 18 (da aka sakaya sunanta) a Gangaren NEPA, Birnin Kabi, babban birnin jihar Kebbi a farkon safiyar yau Juma’a.
DSP Nafi’u Abubakar, jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda, ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Birnin Kabi.
Ya ce jami'a 'yan sanda sun yi duk mai yiwuwa don ceto yarinyar amma abin ya faskara
Abubakar ya shawarci jama'a da akoyaushe su dinga kai rahoton duk abinda ba su amince da shi ba, domin hakan zai taimaka wajen yakar ayukkan ta'addanci.
An kuma gano cewa mahaifin yarinyar da aka sace, Faruq Mohammed jami'in Hukumar Tsaro ta (NSCDC), ta Jihar Kabi ne.
Da yake magana a wata hira da manema labarai, Mohammed, ya ce ‘yan bindigar sun shigo unguwar ne kwaram
“Lokacin da suka zo gidana, na lura tare da jiro hayaniya kuma na fahimci cewa wani abu da ba daidai ba da ke shirin aukuwa.
“Ina da hanyoyi biyu a gidana: daya a gaba yayin da kuma dayar ke cikin gareji.
“Na yanke shawarar cewa ya kamata mu fita ta cikin gareji; cikin rashin sa'a, da bude kofar, sai muka hadu da daya daga cikin 'yan fashin dauke da muggan makamai a gefen motata, cikin hanzari muka nemi wata hanya sannan muka tsallaka zuwa gidan makwabta.
“Yan fashin sun kutsa cikin gida na suka fara bincike daki daki. abin takaici, ‘yata tana kwance a dakinta, lokacin da suka kwankwasa ta bude dakin sai suka dauke ta suka tafi da ita.”
Wata majiya mai tushe ta ce 'yan fashin sun kuma kai hari gidan wani Malam Sanusi Nagoru wanda ya yi jaruntakar tare da biyu daga cikin 'yan ta'addan kuma ya fi karfin su, ya kara da cewa mutumin ya nemi taimako daga wasu mutane.
Majiyar ta ce, babu wanda ya ba shi goyon baya don fatattakar 'yan bindigar, ta kara da cewa ba shi da wani zabi da ya wuce ya gudu da ransa.
“Da ya ga wasu‘ yan fashi sun zo su taimaka musu, sai mutumin ya ture ya ture wadannan ‘yan fashin, ya ranta a na kare.
Daya daga cikin matansa ta zo ta toshe kofar don ta hana barayin shiga babbar hanyar shiga.
Majiyar ta kara da cewa, ''Gani hakan ya sa suka bude wuta suka harbe ta a cinya, wacce yanzu haka ke amsar magani a Cibiyar Kiyon Lafiya Ta Tarayya (FMC) da ke Birnin Kabi." 

Comments

Wadanda aka fi karantawa

National Directorate of Employment (NDE) Disburses 100,000 as a Loan to 108 Agricultural Empowerment Scheme Beneficiaries in Sokoto

The state Coordinator of the agency said this was to enable the beneficiaries to be self reliant and contribute their quota to the development of the country. She said the programme was a combined orientation made up of 108 beneficiaries of Agricultural Empowerment Scheme, Community Based Agricultural Empowerment Scheme, Sustainable Agricultural Development Empowerment Scheme and Graduate Agricultural Empowerment Scheme that were given loans of N100, 000 each. Mrs. Danmallam added that the beneficiaries are graduates of NDE agricultural Extension, Poultry and Vegetable production. She said the money disbursed to them was a loan facility which would attract a single digit simple interest rate of 9 % and will have a moratorium of six months before beneficiaries will start paying back and it is repayable in three years.  Therefore, urged the them to ensure timely repayment to enable other unemployed persons to also benefit. In his goodwill message, ...

Wata Mota Cike Da Harsasan Bindiga Ta Fada Rami A Garin Awka Na Jahar Imo

Hankalin jama'a yayi matukar tashi a jiya Lahadi biyo bayan gano wata babbar mota cike da harsasai masu rai a birnin Anacha na jahar Imo da ke kudu maso gabashin tarayyar Najeriya. Rahotannin da suka shigo muna na cewa jami'an tsaron cikin hanzari sun afkawa garin na kasuwanci domin daukar matakin gaggawa kan lamarin.  Babbar motar wadda ke dauke da kwaliyoyin harsasai masu rai ta fada cikin wani rami da ke kan titi, inda dukan harsasan suka zube. Wata majiya da ta tabbatar da faruwar lamarin ta ce: “Motar ta fadi, kuma duk titin na cike da harsasai.  Wasu yaran ma sun debi wasu da hannayensu suka gudu, kafin jami’an tsaro su iso wurin. ”  Majiyar ta ci gaba da bayyana cewa direban babbar motar da mai yi masa hidima sun yi watsi da motar bayan hatsarin ya faru, inda suka yi batan dabo zuwa inda ba a sani ba. Amma wata majiyar ta ce ‘yan sanda sun cafke direban. “Lamarin ya jawo jami'an tsaro masu yawa zuwa yankin hanyar Awka da da safiyar yau. 'Yan sanda sun...

Biden Ya Doke Trump A Georgia Da Ratar Kuri'u 12,284

 An kammala kirga kuri'un jahar Georgia da ake takaddama kan ta, in da Joe Biden ya lashe jahar da rata mai yawa. Jahar Atlanta Georgia mai yawan kuri'u miliyan biyar da doriya ta zama sha kallo a idon duniya ganin yadda shugaba Donald Trump ya yi zargin shi ne ya samu nasara a jahar kuma ya nemi sai an sake kirga dukan kurin'un da aka kada. A jiya alhamis da yamma ne aka kammala lissafin da ya kwashe kusan fiye da mako daya a na yi, in da ofishin sakataren gwamnatin jahar ya fitar da wannan sanarwa. Ofishin Brad Raffensperger ya bayyana cewa bayan sake kirga dukan kuri'un da hannu, sakamakon da aka samu tun farko yana nan bai sauya ba. Joe Biden ya doke Donald Trump da yawan kuri'u 12,284, yayin da shugaba Donald Trump ya samu 1,872.

An Ruguza Makarantar Malam Abduljabbar Kano

Dazu dazun nan gwamnatin jahar Kanon ta tura jami'an ma'aikatar lura da tsarin filaye in da ta ruguza makarantar Malam Abduljabbar. Gwamnatin dai ta taba bayyana cewa filin da ya ke amfani da shi haramtacce ne, in da ta kai ga kwace shi tare da bada umurnin gudanar da wasu muhimman ayukka a wurin. Dangantaka dai ta yi tsami tsakanin gwamnatin jahar Kano da Abduljabbar in da a ranar laraba sakataren watsa labaran gwamnatin jahar, Muhammad Garba ya bayar da sanarwar rufe masallacin Malam Abduljabbar tare da hana masa gudanar da wa'azi baki daya. In da ta ce hakan na da alaka da irin yadda ya ke tunzura jama'a a kalaman da ya ke amfani da su a lokacin da ya ke da'awa.

Gunmen Abducted 11 FAAN Staff In Kaduna

A group of gunmen yesterday attacked the residences of the Federal Airport Authority of Nigeria Kaduna. Reports say gunmen stormed the compound and abducted at least 11 people. Recent reports suggest that the bandits also abducted a staff of  Nigerian Airspace Management Agency NAMA, his wife, a National Meteorological Agency (NIMET) official and his children.Their whereabouts are still unknown. Kidnappings are common in Nigeria today, and almost every morning there are reports of killings or kidnappings for ransom. Last week Nigerian President Muhammadu Buhari vowed to end abduction in Nigeria but for all indications his words were not effective.

The Nigerian Governors Forum Describe The Militant Attack On Benue State Governor As Shocking

The Nigerian Governors Forum (NGF) has described the militant attack on the Benue State governor as "shocking" and "scary".  Governor Samuel Ortom's delegation was attacked by gunmen on Saturday on the Makurdi-Gboko road, when he visited his farm.  In a statement issued by the group's chairman and Ekiti State Governor Kayode Fayemi on Sunday, the NGF congratulated Ortom for the escape from the attack which it said was "scary and offensive".  Inspector General of Police Mohammed Adamu also condemned the attack and ordered that security be beefed up on the governor and an investigation launched.  "The NGF has said in a loud voice that efforts to rehabilitate Benue State will not succeed," the statement said.  "One of the relatives of a former governor of the state was recently killed. This kind of act of violence must be stopped for whatever reason to kill the people of Benue."

Burtaniya Ta Kakabawa Bankunan Rasha da Mahukuntan Kasar Takunkumin Tattalin Arziki Mafi Girma A Tarihi

Getty images Firaministan Burtaniya, Boris Johnson ya sanar da sakawa Rasha takunkumi mafi tsanani a bangaren tattalin arziki da Rasha ta taba gani, tun bayan da ta mamaye Ukraine. Da yake magana a zauren majalisar, firaministan ya ce za a daskarar da duk wasu manyan bankunan kasar Rasha da kuma cire su daga tsarin kudi na Burtaniya.  Har ila yau, za a dakatar da kamfanin jiragen saman Rasha na Aeroflot sauka a kasar Birtaniya. Mista Johnson ya shaidawa majalisar dokokin kasar a yammacin ranar almais din makon nan cewa, shugaban kasar Rasha Vladimir Putin "mai cin zali ne mai zubar da jini, don haka zai yabawa aya zakinta".

Yahaya Bello Ya Caccaki Buhari

Da ya ke jawabi a lokacin da ake gudanar da shirin zaben fitar da gwani, gwamnan jahar Kogi Yahaya Bello ya nemi a zabe shi domin ya magance matsalar tsaro da karancin ilmi da ake fama da su yanzu haka a Najeriya. Ya ce, "akwai takaici ace wai yanzu malaman jami'a suna ci gaba da yajin aiki, dalibai na zaune a gida kuma an kasa magance wannan matsala mai saukin magancewa". Yahaya Bello wanda ya ce ba zai jaye ma kowa a neman tikitin shugaban kasa, ya kara da cewa shi matashi ne kuma matasa ya kamata a ba dama su mulki kasar nan ba tsofaffi da suka gaji ba. Ya yabawa shugaba Buhari akan saka hannu a kan dokar ba matasa damar tsayawa takara, in da ya ce abu ne mai kyau. Ya yi kira ga mata da sauran 'yan Najeriya da ya ce ana zalunta da su zabe shi. Dan takarar ya ce "yanzu haka babu tsaro ko kadan kuma an kyale, ana kashe mutane ana kona mu su dukiya kuma ana kallo an zura ido".

Binani Ta Zama Mace Ta Farko Da AKa Zaɓa Gwamna A Najeriya

A wani abinda ba saban ba, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Sanata Aisha Dahiru, wacce aka fi sani da Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen gwamnan jahar Adamawa. Kwamishinan zaɓen jahar Adamawa, Farfesa Hudu Yunus Ari, ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ana tsakiyar tattara sakamakon zaɓen. An bayyana sakamako daga ƙananan hukumomi 10 cikin 20 yayin da aka dage ci gaba da bayyana sakamakon zaɓen har zuwa karfe 11 na safe. Sai dai Ari ya sanar da sakamakon ƙarshe awa ɗaya kafin lokacin da aka tsara. Gwamnan jahar Ahmadu Fintiri na jam'iyyar PDP ne ke kan gaba kafin a bayyana hakan. Wasu magoya bayan jam’iyyar PDP a zauren sun nuna rashin amincewarsu da dalilin da ya sa kwamishinan zaɓe ya sanar da sakamakon maimakon baturen tattara sakamakon zaɓe a al'adance.