Skip to main content

Posts

Ko Kun San Yadda Gidajen Samudawa Su Ke?

Samudawa su ne mutanen Annabi Saleh (AS) waɗanda ke da girman jiki da tsawo tamkar bishiyar dabino.   Waɗannan wasu daga gidajen Samudawa ne da suka rage a halin yanzu. Ana kiran wajen da suna (Mada’in Salih) ko Al-Hijr da Larabci,  (ٱلْحِجْر‎‎). Yankin na nan a Al-‘Ula cikin lardin Madina a Hejaz, ta ƙasar Saudiyya. A shekarar 2008, Hukumar Kula Da Adana Kayan Tarihi Ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO) ta ayyana Mada’in Salih  a matsayin wani wajen da take girmamawa, wurin tarihi na Hegra  na nan nisan kilomita 20 arewa da garin Al-‘Ula, tafiyar mil 250 arewa maso yammacin birnin Madina. Samudawa sun wanzu shekaru ɗari bakwai da goma sha biyar kafin haihuwar Annabi Isa (AS). Mutane daga sassa daban-daban na duniya kan ziyarci wurin, domin ganin ikon Allah.

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane Da Dama A Filato

Rahotanni sun ce an kashe mutane da dama tare da ƙona gidaje a rikicin da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a yankin Mai Tumbi da ke ƙaramar hukumar Mangu a jihar Filato. Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce tuni da aka tura ‘yan sanda domin tabbatar da zaman lafiya a yankin da rikincin ya shafa Babban Daraktan Hukumar Tabbatar Da Wanzuwar Zaman Lafiya a Jihar Filato Joseph Lengmang, ya yi Allah wadai da lamarin, inda ya ce sun yi matuƙar baƙin ciki da yadda lamarin ya faru, inda rahotanni masu tayar da hankali suka nuna cewa matsalar tsaro ta tabarbare a yankin, lamarin da ya yi sanadin rasa rayuwa da dukiya mai ɗimbin yawa.

An Ɗaure Wani Ɗan Jaridar Rasha Kan Sukar Putin

Wata kotu a kasar Rasha ta yankewa ɗan jarida hukuncin daurin shekaru shida a gidan yari bisa zargin sa da yin kira da a hambarar da gwamnatin shugaba Vladimir Putin bayan mamayar da ya yi ma ƙasar Ukraine a bara. Shafin yanar gizo na ‘yan shafin yanar gizo na jami'an tsaron 'yan sanda na OVD Info   ya ruwaito ranar Juma’a cewa, an kama Kirill Akimov, mai shekaru 52 a watan Yuni, bisa zargin yin kiraye-kirayen da ka iya kai wa ga tashin hankali yayin gabatar da shiri a wani gidan rediyo a ranar 14 ga Maris, 2022.  Akimov, wanda ya fito daga Jamhuriyar Mordovia ta tsakiyar Rasha, mai tazarar kilomita 400 gabas da birnin Moscow. Kotun soji da ke Yekaterinburg a ranar Laraba ta samu Akimov da laifuffuka biyu na ingiza jama'a su yi bore da kuma aikata ta’addanci, a cewar wata kotu.

Binani Ta Zama Mace Ta Farko Da AKa Zaɓa Gwamna A Najeriya

A wani abinda ba saban ba, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana Sanata Aisha Dahiru, wacce aka fi sani da Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen gwamnan jahar Adamawa. Kwamishinan zaɓen jahar Adamawa, Farfesa Hudu Yunus Ari, ya ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ana tsakiyar tattara sakamakon zaɓen. An bayyana sakamako daga ƙananan hukumomi 10 cikin 20 yayin da aka dage ci gaba da bayyana sakamakon zaɓen har zuwa karfe 11 na safe. Sai dai Ari ya sanar da sakamakon ƙarshe awa ɗaya kafin lokacin da aka tsara. Gwamnan jahar Ahmadu Fintiri na jam'iyyar PDP ne ke kan gaba kafin a bayyana hakan. Wasu magoya bayan jam’iyyar PDP a zauren sun nuna rashin amincewarsu da dalilin da ya sa kwamishinan zaɓe ya sanar da sakamakon maimakon baturen tattara sakamakon zaɓe a al'adance.

Halin Da Ake Ciki Kan Yunƙurin Juyin Mulki A Sudan

Jami'an Ɗaukin Gaggawa don Tallafa ma Tsaro a Sudan na Rapid Support Forces (RSF) a yau asabar sun ce sun ƙwace iko da fadar shugaban ƙasa da gidan hafsan hafsoshin soji da babban filin jirgin sauka da tashin jiragen sama a birnin Khartoum a wani yunƙurin juyin mulki da aka yi a lokacin da rikici ya ɓarke tsananinsu da sojoji. Rundunar ta RSF wacce ta zargi sojojin da fara kai mata hari, ta kuma ce sun ƙwace tashoshin jiragen sama a arewacin garin Merowe da kuma El-Obeid a yammacin ƙasar. Rundunar sojin saman Sudan na ci gaba da fatattakar mayaƙan RSF, a cewar wata sanarwa rundunar.   Wasu gidajen talabijin sun nuna wani jirgin soji a sararin samaniyar birnin Khartoum, amma Tantabara News ba ta tabbatar da sahihancin labarin. Rahotanni da ke shigo muna yanzu haka na bayyana cewa ana iya jin ƙarar harbe-harbe a sassa da dama na birnin Khartoum inda wasu shaidun gani da ido da ke bayar da rahoton harbe-harbe a garuruwan da ke makwabtaka da su, lamarin da ya sa ake fa...

Iran Ta Sha Alwashin Murƙushe Masu Tallata Manufar Cire Hijabi

A ranar Asabar 15 ga watan Afrilun da ya gabata ne mataimakin babban lauyan ƙasar Iran ya bayyana cewa, za a gurfanar da mutanen da ke ƙarfafa mata gwiwar cire hijabi a gaban kotunan laifuka, kuma ba za su sami damar daukaka ƙara kan duk wani hukunci da aka yanke musu ba. Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar mata da ke bijirewa dokokin sanya hijabi da Iran ta sanya, inda suke bayyana a manyan kantuna da gidajen cin abinci da shaguna da sauran wuraren taruwar jama'a.  A cikin 'yan watannin nan wasu mata masu fafutuka sun fito fili sun yaɗa hotunan kansu a shafukan sada zumunta ba tare da lullubi ba. Jami'an tsaron 'yan sandan Iran a ranar Asabar ɗin makon jiya, sun sanya na'urorin ɗaukar hoto a wuraren taruwar jama'a don tantancewa da kuma hukunta matan da aka gano ba su sanye da hijabi, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na Iran suka ruwaito.   Kamfanin dillancin kabaran Reuters ya ruwaito mataimakin babban lauyan gwamnatin ƙa...

Wanene Ɗan Jarida?

Ɗan jarida mutum ne kamar kowa, sai dai tunaninsa da manufofinsa kan tafi daidai ne kawai da ra'ayin MASU SAURARO ta fuskokin da suka shafi aikinsa. Ya zama mai wakiltar waɗanda ba su da baki ne ko kafafuwan zuwa, kuma idanuwan talakawa a kowane lokaci. Idan ka nuna ma sa launi shuɗi, ƙoƙarin ya ke ya tabbatar da launin nan shuɗi ne ziryan ko yana da garwaye? Idan ka ce ma sa labarin abu kaza ya faru, ba zai ce a'a ba kuma ba zai ce eh ba, aikinsa shi ne TABBATARWA . Idan mai sauraro namiji ne ko mace ko mai ra'ayin wani addini ko akida ko mai kuɗi ko talaka, ɗan jarida kan GIRMAMA kowa, kuma zai ɗauki kowa a matsayin DAIDAI ta fuskar ba su damar bayyana ra'ayoyinsu. Ɗan jarida kan tafi da zamani, ya kuma rungumi fasahar da ƘIRƘIRA ta kawo domin tafiya daidai lokaci. A kowace marra GASKIYA ita ce madogarar ɗan jarida, kuma wannan kan ƙara sa masu sauraro su amince da shi. Amma kuma, dole ne ɗan jarida ya zama MAI IKON KANSA , ba zai yi ma kowa alfarma b...

Dalar Amurka Na Fuskantar Barazanar Durkushewa

Shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya soki kasar Amurka akan irin rawar da dala ke takawa a tattalin arzikin duniya tare da yin kakkausar suka ga asusun lamuni na duniya na IMF. Lula ya yi waɗannan kalamai a wata ziyarar aiki da ya kai Chana, jiya Alhamis a birnin Shanghai a wani bikin kaddamar da takwaransa, Dilma Rousseff a matsayin sabuwar shugabar bankin raya kasashen BRICS, da gamayyar kasashenn Brazil da Rasha da Indiya da Chana da kuma Afirka ta Kudu suka samar. "Me ya sa kowace ƙasa za a danganta da dala don kasuwanci? Wanene ya yanke shawarar dala za ta zama kuɗin duniya?"  Ya ƙara da cewa me yasa banki kamar bankin BRICS ba zai iya samun kuɗin da zai gudanar da hulɗar kasuwanci tsakanin Brazil da Chana ba, da ma sauran ƙasashen duniya? Ya ce yana mamakin yadda ƙasashe cike da rauni  su ke bin sawun amfani da dala wajen gudanar da kasuwanci alhali suna iya hakan da kuɗaɗensu. A wata ganawa tsakanin sa da shugaban Chana Xi Jinping, da kuma ya ...

Tinubu Na Gaban Tambuwal A Sokoto

Asiwaju Bola Tinubu, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, ya ba Atiku Abubakar, ɗan takarar jam’iyyar PDP a jihar Sokoto rata a jahar.   Duk da cewa akwai kananan hukumomi 23 a jihar, Tinubu ya tattara mafi yawan kuri’u a kananan hukumomi 10. Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya samu kuri’u 101,608, Alhaji Atiku Abubakar ya samu kuri’u 98,080 yayin da Sanata Rabi’u Kwankwaso na jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP) ya zo na uku da kuri’u 314 sannan Peter Obi na jam’iyyar Labour ya samu kuri’u 171. Kananan Hukumomin Da Aka Samu Sakamakonsu TURETA  Waɗanda aka yi ma rajita: 40,746  Waɗanda aka tantance: 16,516  APC 7, 684  LP.  1  NNPP.  9  PDP.  8, 144  KWARE  Waɗanda aka yi ma rajita 74,056  Waɗanda aka tantance 24,776  APC 10,485  LP.  63  NNPP.  11  PDP.  12,242  BODINGA  Waɗanda aka yi ma rajita 86,139  Waɗanda aka tantance 28,054  A 1 ...

Sakamakon Zaɓen Shugaban Ƙasa Kai Tsaye

Za mu ci gaba da kawo muku sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisar dokoki na ƙasa. Hoto: BBC Hausa